fidelitybank

An ɗaure wanda ake zargi da satar kuɗi

Date:

Wata Kotu da ke Kubwa a Abuja, ta bayar da umarnin a tsare Abba Mohammed a gidan gyaran hali bisa zargin sata.

Alkalin kotun, Muhammad Wakili ya ba da umarnin, bayan Mohammed ya amsa laifin da ake zarginsa da shi.

Wakili, ya dage ci gaba da sauraron karar har zuwa ranar 9 ga watan Oktoba domin yanke hukunci.

‘Yan sandan dai sun tuhumi wanda ake tuhuma da laifin aikata laifuka da kuma sata.

Tun da farko, Lauyan masu shigar da kara, SP Babajide Olanipekun, ya shaida wa kotun cewa Mohammed ya shiga wani shago da ke kan titin Gado Nasko, Kubwa, Abuja, da fakewa da siyan bututun iskar gas a ranar 11 ga Satumba.

Olanipekun ya ce Mohammed ya saci kudi N23,500 daga hannun wani Uchenna Madugba, amma yayin da yake kokarin tserewa, an kama shi.

Lauyan mai shigar da kara ya ce an kwato kudaden ne daga hannun Mohammed, inda ya kara da cewa laifin ya saba wa sashi na 348 da 288 na kundin laifuffuka.

Sashi na 288 ya ce duk wanda ya yi sata za a yanke masa hukuncin daurin shekara bakwai ko tara ko duka biyun. (NAN)

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp