fidelitybank

An ɗaure Matashin Kaduna da ya damfari mutane a Facebook

Date:

An yanke wa wani mutum da ake tuhuma mai suna Miracle Ezeochia, hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari, saboda damfarar wasu mutane da ba a san ko su wanene ba a Facebook.

Wata babbar kotun jihar Kaduna da ke zamanta a Kaduna a ranar Larabar, ta samu Ezeochia da laifin zamba ta hanyar damfara.

Rundunar shiyyar Kaduna ta Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) ta gurfanar da Ezeochhia a gaban mai shari’a N. U. Sadiq.

A wata sanarwa da hukumar EFCC ta fitar a shafinta na sada zumunta da muhawara, ta ce ta samu rahoton sirri kan ayyukan wasu mutane da ake zargi da damfarar yanar gizo a Kaduna, inda ta bayyana cewa daga baya an kama wanda ake tuhuma a wani samame da ta kai.

Yayin da ya ke nazarin na’urarsa, an gano cewa Ezeochia ya bude shafukan Facebook da Instagram dauke da hotuna da sunayen Muhammed Malik daga Qatar da Lucas James Williams, wadanda ya yi amfani da su wajen tattaunawa da mutane da dama, inda aka ce daya daga cikinsu ya karkatar da dala 150.

A cewar tuhumar, Ezeochia, a wani lokaci a watan Oktoba 2022, a Kaduna, ya gabatar da kansa a matsayin Muhammed Malik a Facebook, kuma a cikin irin wannan zato, ya damfari Malik Abdul Haseed kudi dala $150, laifin da ya saba wa sashi na 308 na dokar. Dokar Penal Code ta Jihar Kaduna, 2017 kuma mai hukunci a karkashin sashe na 309 na wannan doka.

Bayan ya amsa laifin da ake tuhumar, lauya mai shigar da kara, M.U. Gadaka, ya roki kotu da ta yanke masa hukuncin da ya dace.

Mai shari’a Sadiq ya yanke hukuncin daurin shekaru biyu a gidan yari tare da zabin biyan tarar N150,000 sannan kuma ya umarce shi da ya bata wayar Tecno POP 7 PRO da $150 ga gwamnatin tarayyar Najeriya.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp