fidelitybank

An ɗauke Kwamishinan ƴan sandan Adamawa

Date:

A ranar Talata ne babban sifeton ‘yan sandan, IGP Usman Baba, ya umarci kwamishinan ‘yan sandan da ke aikin zabe a jihar Adamawa, Mohammed Barde, da ya janye daga jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar, Muyiwa Adejobi, wanda ya bayyana hakan yayin ganawa da manema labarai a ranar Talata, ya ce umarnin ya fara aiki nan take.

Adejobi ya ce IGP din ya kuma umurci kwamishinan ‘yan sandan jihar Gombe, CP Etim Equa da ya gaggauta zuwa jihar Adamawa domin tabbatar da tsaro a zaben gwamnan da ba a kammala ba.

Ya ce, “IGP ya bayar da umarnin cewa kwamishinan ‘yan sanda kan harkokin tsaro a jihar Adamawa, CP Barde ya janye daga jihar Adamawa, shi kuma kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Gombe, CP Etim Equa ya garzaya Adamawa cikin gaggawa, domin ku je ku sa ido kan zaben da bayar da bayanan da suka dace da kuma tabbatar da cewa tsarin ya yi nasara.”

A halin da ake ciki, an tsaurara matakan tsaro a cibiyar tattara sakamakon zaben jihar Adamawa yayin da jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ke ci gaba da zama kwanaki bayan da hukumar ta dakatar da atisayen.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp