fidelitybank

An ɗage zaman Majalisar dokoki cikin rudani kan rikicin Rivers

Date:

Majalisar dattawa ta ɗage tattaunawa kan ƙudirin farko da za su tafka muhawara a zamansu na yau game da amincewa da dokar ta-ɓaci a jihar Rivers ba tare da bayar da dalilin jinkirin ba.

A yanzu majalisar za ta zauna kan wannan batu da ƙarfe uku na rana.

An yi tsammanin za a tafka muhawara kan ƙudirin wanda shugaban masu rinjaye na majalisar dattawa, Opeyemi Bamidele ya gabatar, da safiya sai dai ƴanmajalisar sun ɗage tattaunawar.

Ƙudirin dai ya bayyana damuwa game da ruruwar tashin hankali da ya jefa jihar Rivers cikin garari tare da haifar da koma-baya a tafiyar da al’amuran gwamnati.

Gidan Talabijin na Channels ya ruwaito cewa kafin dokar ta-ɓacin ta soma aiki, dole ne sai ƙudirin ya samu goyon bayan kashi ɗaya bisa uku na ƴanmajalisar – 73 cikin sanatoci 109.

A yanzu dai hankalin ƴan Najeriya ya karkata kan majalisar dokokin Najeriya domin jin yadda za ta kaya game da dokar ta-ɓacin da Shugaba Tinubu ya ƙaƙaba a Rivers ta tsawon wata shida.

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp