fidelitybank

An ƙarawa ƙananan ƴan sanda 21,039 girma a Najeriya

Date:

Sufeto-Janar na ‘yan sanda, IGP Usman Alkali Baba, ya kara wa kananan ‘yan sanda 21,039 karin girma, wadanda aka yi musu karin girma tun a shekarar 2017 ko kafin nan.

A bangaren wadanda suka ci gajiyar tallafin, Sajan 20,572 aka kara musu girma zuwa mukamin Sufeto, yayin da Kofur 324 aka mayar da su Sajan.

Haka kuma an karawa ‘yan sanda 143 mukamin Kofur.

A cewar mai magana da yawun ‘yan sandan Olumuyiwa Adejobi, wannan karin girma na daga cikin kokarin da ake yi na inganta walwalarsu.

Haka kuma ana nufin kara kwarin gwiwar ma’aikata, da nufin sake mayar da rundunar, don samun ingantacciyar aiki.

IGP din ya ci gaba da cewa, karin girma ga jami’an na daya daga cikin ayyukan bunkasa ma’aikata, don tabbatar da cewa, an kara wa ma’aikatan da suka cancanta karin girma yadda ya kamata, domin karfafa kwazon aiki, da kuma kara sanya al’adar kwarewa da kwazo wajen gudanar da ayyuka.

www.najnew

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp