fidelitybank

Amurka za ta sayarwa da Najeriya makamai masu kai hari

Date:

Amurka ta amince ta sayar wa Najeriya makamai da kudinsu ya kai na dala biliyan daya da zummar karfafa yaki da kungiyoyi masu rike da makamai.

A wata sanarwa da hukumar hadin kai game da tsaro ta Amurka ta fitar, ta ce, Najeriya ta bukaci sayen jiragen masu saukar Ungulu guda 12 masu kai hare-hare da makami, inda aka nufa ba tare da matsala ba.

Amurka ta ce, daga yanzu Najeriya ba za ta fuskanci wata matsala ba wajen sayen makamai daga wurin ta ba.

Sai dai a na sa rai wannan batun zai dauki akalla shekaru biyar kafin a kammala shi, domin kuwa zai hada da horas da dakarun tsaron Najeriya kan yadda za su yi aiki da makaman da kuma kauce wa kai hari kan fararen hula.

Wannan ne karo na biyu da Amurka ke sayar wa Najeriya makamai cikin shekaru biyar.

A baya gwamnatin Barack Obama ta ki sayar wa Najeriya makamai bisa zargin take hakkin dan adam.

Sai dai a shekarar 2017, gwamnatin Donald Trump ta amince ta sayar wa Najeriya jiragen yaki samfurin Super Tucano guda 12.

A shekarar da ta gabata ne aka kai jiragen Najeriya.

current eggon news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulÉ—a da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu É—auki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta É—aukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu Æ™awayen Amurka za su É—anÉ—anar kuÉ—arsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...
X whatsapp