fidelitybank

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Date:

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da kimarsu ta kai kusan dala miliyan 10, waɗanda hukumar tallafawa ƙasashen duniya ta Amurka (USAID) ta saya domin rabawa asibitoci a ƙasashen duniya.

An adana magungunan ne a wani dakin ajiya da ke ƙasar Belgium, inda aka shirya aikewa da su zuwa ƙasashen da samun magungunan ke da wuya.

Sai dai tun bayan rufe hukumar USAID da gwamnatin shugaba Donald Trump ta yi a bana, ayyukanta da shirin rabon kaya suka tsaya cik.

Gwamnatin Amurka ta ce an yanke shawarar lalata magungunan ne saboda dokoki da ƙa’idodin Amurka da bai goyon bayan zubar da ciki.

Haka kuma, gwamnati ta ce fiye da kashi 30 na magungunan sun kusan lalacewa kuma sake musu kwali da sake sayar da su zai iya cin miliyoyi.

Sanata Jeanne Shaheen daga jihar New Hampshire ta gabatar da kudirin doka domin dakatar da lalata magungunan inda ta ce magungunan suna da muhimmanci gare ta da kuma sauran mata saboda tasirin da zai iya yi ga lafiyar mata a kasashe masu ƙaramin karfi.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp