Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da kimarsu ta kai kusan dala miliyan 10, waɗanda hukumar tallafawa ƙasashen duniya ta Amurka (USAID) ta saya domin rabawa asibitoci a ƙasashen duniya.
An adana magungunan ne a wani dakin ajiya da ke ƙasar Belgium, inda aka shirya aikewa da su zuwa ƙasashen da samun magungunan ke da wuya.
Sai dai tun bayan rufe hukumar USAID da gwamnatin shugaba Donald Trump ta yi a bana, ayyukanta da shirin rabon kaya suka tsaya cik.
Gwamnatin Amurka ta ce an yanke shawarar lalata magungunan ne saboda dokoki da ƙa’idodin Amurka da bai goyon bayan zubar da ciki.
Haka kuma, gwamnati ta ce fiye da kashi 30 na magungunan sun kusan lalacewa kuma sake musu kwali da sake sayar da su zai iya cin miliyoyi.
Sanata Jeanne Shaheen daga jihar New Hampshire ta gabatar da kudirin doka domin dakatar da lalata magungunan inda ta ce magungunan suna da muhimmanci gare ta da kuma sauran mata saboda tasirin da zai iya yi ga lafiyar mata a kasashe masu ƙaramin karfi.