fidelitybank

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Date:

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da kimarsu ta kai kusan dala miliyan 10, waɗanda hukumar tallafawa ƙasashen duniya ta Amurka (USAID) ta saya domin rabawa asibitoci a ƙasashen duniya.

An adana magungunan ne a wani dakin ajiya da ke ƙasar Belgium, inda aka shirya aikewa da su zuwa ƙasashen da samun magungunan ke da wuya.

Sai dai tun bayan rufe hukumar USAID da gwamnatin shugaba Donald Trump ta yi a bana, ayyukanta da shirin rabon kaya suka tsaya cik.

Gwamnatin Amurka ta ce an yanke shawarar lalata magungunan ne saboda dokoki da ƙa’idodin Amurka da bai goyon bayan zubar da ciki.

Haka kuma, gwamnati ta ce fiye da kashi 30 na magungunan sun kusan lalacewa kuma sake musu kwali da sake sayar da su zai iya cin miliyoyi.

Sanata Jeanne Shaheen daga jihar New Hampshire ta gabatar da kudirin doka domin dakatar da lalata magungunan inda ta ce magungunan suna da muhimmanci gare ta da kuma sauran mata saboda tasirin da zai iya yi ga lafiyar mata a kasashe masu ƙaramin karfi.

sspdf news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaƙi – Thailand

Thailand ta gargaɗi cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar ƙasar Falasɗinawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin ƙai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haɗin gwiwar...
X whatsapp