fidelitybank

Amurka za ta kwashe sojojin ta a kasar Nijar

Date:

Amurka na shirin kwashe duka dakarunta daga Jamhuriyar Nijar, domin kawo ƙarshen yaƙin da suke yi da masu iƙirarin jihadi.

A ranar Juma’a ne Amurka ta bayyana cewa za ta rufe sansanin jiragenta marasa matuƙa a kusa da Agadez.

Shugabannin mulkin sojin Nijar sun ƙulla sabon ƙawance da ƙasar Rasha, bayan hamɓarar da gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum a shekarar da ta gabata.

Nijar ta kasance ƙasar da Amurka ta dogara da ita wajen gudanar da ayyukanta na yaƙi da masu iƙirarin jihadi.

Nan gaba kaɗan ne tawagar wakilan Amurka za su je birnin Yamai domin shirya yadda za su kwashe dakarun ƙasar fiye da 1,000.

Hakan na zuwa ne bayan tattaunawar da ta gudana a birnin Washington tsakanin mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell, da firaministan Nijar ɗin Ali Lamine Zeine.

nigeria news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp