Amurka na shirin kwashe duka dakarunta daga Jamhuriyar Nijar, domin kawo ƙarshen yaƙin da suke yi da masu iƙirarin jihadi.
A ranar Juma’a ne Amurka ta bayyana cewa za ta rufe sansanin jiragenta marasa matuƙa a kusa da Agadez.
Shugabannin mulkin sojin Nijar sun ƙulla sabon ƙawance da ƙasar Rasha, bayan hamɓarar da gwamnatin farar hula ta Mohamed Bazoum a shekarar da ta gabata.
Nijar ta kasance ƙasar da Amurka ta dogara da ita wajen gudanar da ayyukanta na yaƙi da masu iƙirarin jihadi.
Nan gaba kaɗan ne tawagar wakilan Amurka za su je birnin Yamai domin shirya yadda za su kwashe dakarun ƙasar fiye da 1,000.
Hakan na zuwa ne bayan tattaunawar da ta gudana a birnin Washington tsakanin mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka Kurt Campbell, da firaministan Nijar ɗin Ali Lamine Zeine.