Firaministan Kanada Justin Trudeau ya ce, ƙasarsa za ta ɗauki irin matakin da Amurka ta ɗauka na ƙaƙaba harajin kashi 25 cikin ɗari kan kayan Amurka.
Mista Trudeau ya ce abin da zai fi zamar wa Amurka alheri shi ne ta haɗa ƙarfi da Kanada ba wai ta wofintar da ita ba.
Ya ce a yau ina sanar da ku cewa Kanada ta dauki matakin mayar da martani na kashi ashirin cikin dari na kayan biliyoyin daloli da ake shigowa da su daga Amurka.
Ita ma Mexico ta bayyana cewa za ta ɗauki mataki, yayin da ita kuwa China ta yi barazanar ɗaukar matakin shari’a kan Amurkar.
Wannan ya biyo bayan ƙarin kashi 25 cikin ɗari da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi ne a kan kayan da ƙasashen uku ke shigarwa Amurka, inda China har ma da ƙarin kashi 10 cikin ɗari ya ƙara lafta mata.