fidelitybank

Amurka za ta baiwa Najeriya dala miliyan 27

Date:

Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya sanar da cewa Najeriya za ta samu dala miliyan 27 a wani ɓangare na tallafin dalar Amurka miliyan 536 da gwamnatin Amurka za ta bai wa ƙasashen Afirka a kudu da hamadar Sahara.

“Wannan tallafin wani ɓangare ne na ƙudurin Amurka na isar da muhimmin taimakon tallafa wa rayuwar al’umma masu rauni a faɗin nahiyar Afirka,” a cewar sanarwar.

Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills, ya bayyana muhimmancin sabon tallafin inda ya ce “Wannan taimakon zai kawo sauyi sosai a rayuwar waɗanda suka fi buƙata a Najeriya da ma nahiyar Afirka baki daya.”

Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka kan tsaron fararen hula da Dimokuradiyya da kare haƙƙokin ɗan’adam, Uzra Zeya ne ya ƙaddamar da shirin tallafin a hukumance inda hakan ya kawo jimillar taimakon jin-kai da Amurka ke bayarwa ga yankin kudu da hamadar Sahara a shekarar kasafin kudi ta 2024 zuwa kusan dala biliyan 3.7.

An yi shirin bayar da tallafin ne don magance buƙatu na gaggawa tsakanin mutane masu rauni a fadin yankin, da suka hada da ƴan gudun hijirar da suka tsere daga yaki da ta’addanci da masu neman mafaka, da ƴan gudun hijira a cikin gida da marasa galihu, da sauran wadanda rikici ya shafa.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp