Ofishin Jakadancin Amurka a Najeriya ya sanar da cewa Najeriya za ta samu dala miliyan 27 a wani ɓangare na tallafin dalar Amurka miliyan 536 da gwamnatin Amurka za ta bai wa ƙasashen Afirka a kudu da hamadar Sahara.
“Wannan tallafin wani ɓangare ne na ƙudurin Amurka na isar da muhimmin taimakon tallafa wa rayuwar al’umma masu rauni a faɗin nahiyar Afirka,” a cewar sanarwar.
Jakadan Amurka a Najeriya, Richard Mills, ya bayyana muhimmancin sabon tallafin inda ya ce “Wannan taimakon zai kawo sauyi sosai a rayuwar waɗanda suka fi buƙata a Najeriya da ma nahiyar Afirka baki daya.”
Mataimakin sakataren harkokin wajen Amurka kan tsaron fararen hula da Dimokuradiyya da kare haƙƙokin ɗan’adam, Uzra Zeya ne ya ƙaddamar da shirin tallafin a hukumance inda hakan ya kawo jimillar taimakon jin-kai da Amurka ke bayarwa ga yankin kudu da hamadar Sahara a shekarar kasafin kudi ta 2024 zuwa kusan dala biliyan 3.7.
An yi shirin bayar da tallafin ne don magance buƙatu na gaggawa tsakanin mutane masu rauni a fadin yankin, da suka hada da ƴan gudun hijirar da suka tsere daga yaki da ta’addanci da masu neman mafaka, da ƴan gudun hijira a cikin gida da marasa galihu, da sauran wadanda rikici ya shafa.