Mataimakiyar shugaban ƙasar Amurka, Kamala Harris ta yi Allah-wadai a mamadin fadar White House da kashe fararen hula a Gaza sakamakon mummunan hari ta sama da Isra’ila ta kai kan wata makaranta a jiya Asabar.
Ms Harris, wadda ita ce kuma ƴar takarar shugabar ƙasa a Jam’iyar Democrats a zaɓen da za a yi a watan Nuwamba, ta ce wannan karon ma an sake kashe fararen hula masu yawa, ta kuma sake nanata kira da a cimma yarjejeniyar tsagaita wuta da sako waɗanda aka yi garkuwa da su a Gaza.
Ta ce Isra’ila na da damar kai wa Hamas hari amman ta yi ammanar cewa yana da matuƙar muhimmaci a kiyaye rayukan fararen hula.
Mutum sama da 70 harin na Isra’ila ya kashe a ginin makarantar inda Falasɗinawa da ke gudun hijira suka fake, kamar yadda darektan wani asibiti ya gaya wa BBC.
Kakakin sojin Isra’ila ya ce, makarantar al-Taba’een da aka kai harin na zaman wata cibiya ta aikin soji ta Hamas da kungiyar Islamic Jihad, zargin da Hamas ta musanta.