fidelitybank

Amurka ta yabawa Kenya yadda ta yi zaɓe

Date:

Ofishin jakadancin Amurka a Kenya ya yaba wa ‘yan kasar Kenya saboda yadda aka gudanar da zabe cikin lumana, sannan ya bukaci dukkan jam’iyyun siyasar kasar da su hada kai su yi aiki tare domin warware dukkan abubuwan da ke damun kasar cikin sauki.

Ofishin ya ce ayyana William Ruto a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasa kuma abu ne mai matukar muhimmanci a siyasar kasar.

Kazalika ofishin ya bukaci shugabannin siyasar kasar da su ci gaba da jan hankalin magoya bayansu a kan zama lafiya da kuma kaucewa dukkan wata fitina.

An ayyana Mr Ruto a matsayin wanda ya samu nasara a zaben shugaban kasar da aka yi inda ya samu 50.9 cikin 100 a kudin da aka kada abin da ya sa ya kayar da abokin takararsa tsohon Firaiminista Raila Odinga.

Wakilan Mr Odina a wasu mazabun sun ba za su iya tabbatar da sahihancin zaben ba sannan kuma wasu Kwamshinonin hukumar zaben sun sanar da sakamakon zaben da ba su tabbatar da sahihancinsa ba.

Mr Ruto ya yi alkawarin aiki tare da ‘yan kasar yana mai cewa sakamakon zaben an yi shi cikin adalci.

An rinka shagulgula bayan sanar da sakamakon zaben, yayin da rahotanni kuma ke cewa an samu barkewar zanga-zanga a wasu yankunan da ke da magoya bayan Mr Odinga. In ji BBC Hausa.

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...
X whatsapp