fidelitybank

Amurka ta yabawa Kenya yadda ta yi zaɓe

Date:

Ofishin jakadancin Amurka a Kenya ya yaba wa ‘yan kasar Kenya saboda yadda aka gudanar da zabe cikin lumana, sannan ya bukaci dukkan jam’iyyun siyasar kasar da su hada kai su yi aiki tare domin warware dukkan abubuwan da ke damun kasar cikin sauki.

Ofishin ya ce ayyana William Ruto a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasa kuma abu ne mai matukar muhimmanci a siyasar kasar.

Kazalika ofishin ya bukaci shugabannin siyasar kasar da su ci gaba da jan hankalin magoya bayansu a kan zama lafiya da kuma kaucewa dukkan wata fitina.

An ayyana Mr Ruto a matsayin wanda ya samu nasara a zaben shugaban kasar da aka yi inda ya samu 50.9 cikin 100 a kudin da aka kada abin da ya sa ya kayar da abokin takararsa tsohon Firaiminista Raila Odinga.

Wakilan Mr Odina a wasu mazabun sun ba za su iya tabbatar da sahihancin zaben ba sannan kuma wasu Kwamshinonin hukumar zaben sun sanar da sakamakon zaben da ba su tabbatar da sahihancinsa ba.

Mr Ruto ya yi alkawarin aiki tare da ‘yan kasar yana mai cewa sakamakon zaben an yi shi cikin adalci.

An rinka shagulgula bayan sanar da sakamakon zaben, yayin da rahotanni kuma ke cewa an samu barkewar zanga-zanga a wasu yankunan da ke da magoya bayan Mr Odinga. In ji BBC Hausa.

www.legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp