Ofishin jakadancin Amurka a Kenya ya yaba wa ‘yan kasar Kenya saboda yadda aka gudanar da zabe cikin lumana, sannan ya bukaci dukkan jam’iyyun siyasar kasar da su hada kai su yi aiki tare domin warware dukkan abubuwan da ke damun kasar cikin sauki.
Ofishin ya ce ayyana William Ruto a matsayin wanda ya ci zaben shugaban kasa kuma abu ne mai matukar muhimmanci a siyasar kasar.
Kazalika ofishin ya bukaci shugabannin siyasar kasar da su ci gaba da jan hankalin magoya bayansu a kan zama lafiya da kuma kaucewa dukkan wata fitina.
An ayyana Mr Ruto a matsayin wanda ya samu nasara a zaben shugaban kasar da aka yi inda ya samu 50.9 cikin 100 a kudin da aka kada abin da ya sa ya kayar da abokin takararsa tsohon Firaiminista Raila Odinga.
Wakilan Mr Odina a wasu mazabun sun ba za su iya tabbatar da sahihancin zaben ba sannan kuma wasu Kwamshinonin hukumar zaben sun sanar da sakamakon zaben da ba su tabbatar da sahihancinsa ba.
Mr Ruto ya yi alkawarin aiki tare da ‘yan kasar yana mai cewa sakamakon zaben an yi shi cikin adalci.
An rinka shagulgula bayan sanar da sakamakon zaben, yayin da rahotanni kuma ke cewa an samu barkewar zanga-zanga a wasu yankunan da ke da magoya bayan Mr Odinga. In ji BBC Hausa.