Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai da hare-haren da Amurka ta kai ƙasar, inda ya ce ba za su lamunci haka ba kuma Iran “za ta yi amfani da duk abin da ya kamata wajen kare kanta”.
“Hare-haren za su haifar da tarin matsaloli. Ya kamata kowane mamba na MDD ya san da wannan abu mai hatsari, rashin mutunta doka da kuma aikata babban laifi,” kamar yadda ya wallafa a shafin X.
Araghchi ya ƙara da cewa Amurka ta “aikata mummunan laifi” kan bil’adama a matsayinta na mamba a kwamitin tsaro na MDD.