fidelitybank

Amurka ta soki Isra’ila a kan yadda ta ke kashe fararen hula a Falasdinu

Date:

Amurka ta soki yadda Isra’ila ke yaƙi a zirin Gaza, a daidai lokacin da aka shiga watanni biyu da ɓarkewar yaƙin tsakaninta da Hamas.

Sakataren harkokin wajen Amurka ya ce Isra’ila ba ta cika alƙawarin da ta ɗauka na kare farar hula a yaƙin da ta ke ƙara zafafawa a Gaza ba, idan aka kwatanta da halinda ake ciki a yanzu.

Anthony Blinken ya shaidawa manema labarai a Washington cewa, akwai matakai da dama da Isra’ila ya kamata ta ɗauka domin tabbatar da cewa Falasdinawa Farar hula sun isa tudun mun tsira cikin nutsuwa.

Mr Blinken ya ce ba wai kawai su isa wurare masu aminci kaɗai ba, har da yi musu bayanin inda ya kamata su nufa, da lokacin da za su tafi, suna buƙatar abubuwa kamar ruwan sha da abinci da magani.

Babban jami’in Majalisar Ɗinkin Duniya, Martin Griffiths ya ce yana fatan buɗe iyakar Isra’ila da Kerem Shalom ka iya sauƙaƙa kai kayan agaji cikin sauri ga Falasdinawa. In ji BBC.

the nation newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp