fidelitybank

Amurka ta sauya wa dakarun ta na Nijar matsuguni

Date:

Gwamnatin Amurka ta dauki matakin sauya wa dakarunta de ke ƙasar Nijar matsuguni bayan juyin mulkin da aka yi a ƙsar.

Mai magana da yawun ma’aikatar tsaro ta Pentagon Sabrina Singh ta ce a mayar da wasu sojojinta da ke sansani na 101 da ke kusa da babban birnin kasar Yamai zuwa sansaninta na 201 da ke Agadez “a matsayin riga-kafi” makonni shida bayan da sojoji suka karɓi mulkin ƙasar.

Misis Singh ta ce wata ƙaramar tawagar sojojin za su ci gaba da zama a sansanin Yamai.

Bayan juyin mulkin da sojoji sukayi a watan Yuli, Amurka ta dakatar da wasu ayyukan agajin da kasashen ketare ke bai wa ƙasar tare da dakatar da horar da sojoji, inda aka killace sojoji a sansanonin.

A hukumance Amurka ba ta kira mamayar da sojoji suka yi a Nijar a matsayin juyin mulki ba, matakin da zai takaita irin taimakon tsaro da Washington za ta iya bai wa kasar da kayayyakin aiki da za a iya turawa ga sojojin.

“Tsarin mu a Nijar bai canza ba. Matsayinmu har yanzu shi ne. Muna fatan za a nemi mafita ta hanyar diflomasiyya, amma babu wata barazana ga jami’an Amurka ko tashin hankali a kasa,” in ji Ms Singh.

Amurka na da a kalla dakaru 1,100 a sansanoninta guda biyu a Nijar.

Sansanin jirage marasa matuka na Agadez mai nisan kilomita 920 daga birnin Yamai.

Ita ma ƙasar Faransa wadda ta kasance tsohuwar ƙasar Nijar ta mulkin mallaka na da dakaru kusan 1,500 a ƙasar.

Sai dai ya zuwa yanzu, Paris ta yi watsi da kiraye-kirayen da shugabannin da suka yi juyin mulki suka yi na su fice daga kasar, lamarin da ya haifar da zanga-zanga yayin da jama’a suka yi sansani a kusa da sansanin.

nigeria news today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp