Wani dan Saudiyya da Amurka ke tuhuma da zama mutum na 20 ciin wadanda suka kai harin 11 ga watan Satumbar 2001 ya shaki iskar ‘yanci bayan da aka sake shi daga gidan yarin Guantanamo Bay, inji ma’aikatar tsaro ta kasar.
Amurka ta saki Mohammed al-Qahtani, mai shekara 46 kuma ta tasa keyarsa zuwa Saudiyya bayan da wani kwamiti ya sake duba batunsa, kuma ya ce babu alamar zai sake zama mai hatsari ga Amurka.
Kwamitin ya jingina sakamakon nasa ne kan abin da ya kira “tabarbarewar lafiyar kwakwalwarsa”.
Bayan da aka kama shi a a 2001 Amurka ta azabtar da shi har ta kai ga ba za a iya gurfanar da shi a gaban shari’a ba. In ji BBC.
Jamai’an gwamnatin Amurka sun ce dama an shirya cewa, Qahtani zai shiga jirgin United Airlines mai lamaba 93 ne, wanda shi ne ya fado a jihar Pennsylvania bayan da wasu wadanda ake tuhuamr ‘yan al Qaeda ne su hudu suka kwace shi daga matukansa a ranar 11 ga watan Satumbar 2001.
Sai dai Amurka ta hana shi bizar shigga kasar a watan Agustan wannan shekarar.