fidelitybank

Amurka ta kakabawa Yahudawa takunkumi bisa cin zarafin Falasdinawa

Date:

Shugaban Amurka Joe Biden ya amince da ƙaƙaba takunkumi kan wasu ‘yan Isra’ila hudu, ƴan kama wuri zauna da ake zargi da cin zarafin Faladinawa a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan.

Biden ya rattaba hannu kan wani babban umarni na zartarwa, yana mai cewa tashe-tashen hankula a Gabar Yamma da Kogin Jordan sun kai matakin da ba za a iya jurewa ba.

Ɗaya daga cikin wadanda matakin ya shafa, ana zarginsa da tayar da tarzoma a garin Huwara na Falasdinu wanda ya yi sanadiyar mutuwar wani mazaunin yankin.

Takunkumin ya hana mutanen shiga dukkan wani kadarorin Amurka da tsarin hada-hadar kudi na Amurka.

Tashe-tashen hankula a Gabar Yamma da Kogin Jordan na karuwa tun bayan da Hamas ta kaddamar da harin da ba a taba gani ba a Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba.

Jami’an Amurka sun ce takunkumin dai-dai yake da wanda ake ƙaƙabawa ƴan ta’adda.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp