Shugaban Amurka Joe Biden ya amince da ƙaƙaba takunkumi kan wasu ‘yan Isra’ila hudu, ƴan kama wuri zauna da ake zargi da cin zarafin Faladinawa a Gaɓar Yamma da Kogin Jordan.
Biden ya rattaba hannu kan wani babban umarni na zartarwa, yana mai cewa tashe-tashen hankula a Gabar Yamma da Kogin Jordan sun kai matakin da ba za a iya jurewa ba.
Ɗaya daga cikin wadanda matakin ya shafa, ana zarginsa da tayar da tarzoma a garin Huwara na Falasdinu wanda ya yi sanadiyar mutuwar wani mazaunin yankin.
Takunkumin ya hana mutanen shiga dukkan wani kadarorin Amurka da tsarin hada-hadar kudi na Amurka.
Tashe-tashen hankula a Gabar Yamma da Kogin Jordan na karuwa tun bayan da Hamas ta kaddamar da harin da ba a taba gani ba a Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba.
Jami’an Amurka sun ce takunkumin dai-dai yake da wanda ake ƙaƙabawa ƴan ta’adda.