Shugaba Amurka Joe Biden ya yabi matukan jirgin da suka harbo balambalan ɗin China da ta kira shi na leƙen asiri a gaɓar teku da ke South Carolina bisa umarninsa.
Ma’aikatar tsaron Amurka na da yakinin cewa balambalan ɗin na yi wa Amurka leken asiri ne, abin da ya sa suka jira har sai da ya ratsa ta kan teku sannan suka harbo shi, don kar ya jikkata mutane.
Karanta Wannan: Ba ma goyon bayan kowa a zaben 2023 – Amurka
Jami’ai a gwamnatin Biden sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa Amurka ta tattauna da China kai-tsaye bayan harbo shi.
Wakilin BBC ya ce, an rufe sararin samaniyar Amurkar da hana jiragen sama ratsa yankin da aka harbo kumbon.
Sojojin Amurka a yanzu na ƙoƙarin tattaro ko gano wasu bayanai a tarkacen balambalan ɗin da ya tarwatse a kan teku.