fidelitybank

Amurka ta haramta amfani da TikTok a ƙasar ta

Date:

TikTok ya bayyana cewa zai ‘daina aiki’ a Amurka daga ranar Lahadi, matuƙar dai gwamnatin shugaba Joe Biden ba ta ɗauki matakin hana dakatar da shi ba.

Hakan na zuwa ne bayan Kotun ƙolin ƙasar, a ranar Juma’a ta amince da matakin Majalisar dokokin Amurka na haramta ayyukan manhajar, har sai idan kamfanin da ya mallaki manhajar – wanda ke da alaƙa da China – ya amince zai sayar da ita ga wani kamfanin Amurka, bisa dalilai na tsaro.

Fadar shugaban Amurka ta White House ta ce ba za ta bayar da umarnin amfani da dokar ba, to amma TikTok ya ce idan har da gaske ne to ya kamata gwamnati ta fitar da sanarwa domin tabbatar wa kamfanonin Apple da Google matsayar tata.

Donald Trump, wanda za a rantsar a matsayin shugaban Amurka a ranar Litinin – ya nuna aniyar ganin ba a tabbatar da haramcin amfani da mahajar ba.

Majalisar Dokokin Amurka ce ta yanke shawarar haramta TikTok a ƙasar ne bisa dalilai na tsaro, inda ta ce akwai yiwuwar gwamnatin China na amfani da manhajar wajen tattara bayanan mutanen Amurka, wanda take amfani da shi wajen yaɗa manufa.

nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp