fidelitybank

Amurka ta haramta amfani da TikTok a ƙasar ta

Date:

TikTok ya bayyana cewa zai ‘daina aiki’ a Amurka daga ranar Lahadi, matuƙar dai gwamnatin shugaba Joe Biden ba ta ɗauki matakin hana dakatar da shi ba.

Hakan na zuwa ne bayan Kotun ƙolin ƙasar, a ranar Juma’a ta amince da matakin Majalisar dokokin Amurka na haramta ayyukan manhajar, har sai idan kamfanin da ya mallaki manhajar – wanda ke da alaƙa da China – ya amince zai sayar da ita ga wani kamfanin Amurka, bisa dalilai na tsaro.

Fadar shugaban Amurka ta White House ta ce ba za ta bayar da umarnin amfani da dokar ba, to amma TikTok ya ce idan har da gaske ne to ya kamata gwamnati ta fitar da sanarwa domin tabbatar wa kamfanonin Apple da Google matsayar tata.

Donald Trump, wanda za a rantsar a matsayin shugaban Amurka a ranar Litinin – ya nuna aniyar ganin ba a tabbatar da haramcin amfani da mahajar ba.

Majalisar Dokokin Amurka ce ta yanke shawarar haramta TikTok a ƙasar ne bisa dalilai na tsaro, inda ta ce akwai yiwuwar gwamnatin China na amfani da manhajar wajen tattara bayanan mutanen Amurka, wanda take amfani da shi wajen yaɗa manufa.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp