fidelitybank

Amurka ta gargaɗi ƴan ƙasarta da su yi taka tsantsan a Najeriya

Date:

Amurka ta fitar da wani gargaɗi ga ‘yan ƙasarta da ke zaune a Najeriya da su kauce wa zuwa manyal otal-otal a ƙasar.

Hakan na ƙunshe cikin wata sanarwar gaggawa da ƙasar ta aike wa ‘ya’yanta mazauna Najeriya ranar Juma’a 3 ga watan Nuwamba.

Sanarwar gargaɗin ta ce ta an ɗauki matakin gargaɗin ne saboda samun bayanan sirri game da yiwuwar kai hari manyan otol-otal a faɗin ƙasar.

Ta buƙaci Amurkawan da ke ƙasar su riƙa lura a manyan otal-otal, da wuraren da suke zaune, su kuma rage bayyana kansu a bainar jama’a, sannan su riƙa bin shawarwarin tafiye-tafiye zuwa Najeriya da Amurkan ke fitar wa kafin su shiga kowane Otal.

Sanarwar ta ce, “Gwamnatin Amurka na sane da sahihan bayanai da ke nuna barazana a man’yan otal-otal a manyan biranen Najeriya”.

“Jami’an tsaron Najeriya na aiki tuƙuru, don magance barazanar”, in ji sanarwar.

haka kuma sanarwar ta fitar da wasu lambobin wayar ofisoshin jakadancinta da ke Abuja da Legas, ga duk Ba’amurken da ke buƙatar taimako.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp