fidelitybank

Amurka ta gano China ta yaɗa cutar Korona da gangan a duniya

Date:

Hukumar leƙen asiri ta Amurka, CIA, ta gabatar da sabon bayani kan binciken da ta yi game da abin da ake ganin ya haddasa annobar Korona (Covid19) a duniya, inda ta ce tana ganin zai fi yuwuwa ƙwayar cutar ta fita ne daga ɗakin bincike na kimiyya saɓanin daga jikin dabbobi.

Kakakin hukumar ya ce bisa ga dukkan alamu ɓullar cutar na da alaƙa da aikin bincike -maimakon a ce haka kawai ta ɓulla, kamar yadda rahoto ya nuna.

To amma kuma hukumar ta CIA ta ce ba ta da cikakken ƙwarin gwiwa a kan hakan.

Shawarar fitar da wannan sakamako ta kasance ɗaya daga cikin matakan da sabon shugaban hukumar ta CIA, John Ratcliffe, wanda Donald Trump ya naɗa ranar Alhamis, ya yi.

Daman tun a lokacin Trump na farko Ratcliffe, wanda a lokacin darekta ne a hukumar samar da tsaro ga shugaban ƙasa, yana da ra’ayin cewa cutar ta ɓulla ne daga ɗakin kimiyya na cibiyar binciken kimiyya ta Wuhan da ke China.

Cibiyar tana da tazarar tafiyar minti 40 ne a mota daga kasuwar da ake sayar da kifi da sauran naman ruwa – inda ake cewa daga kasuwar ne cutar ta ɓulla.

China dai a kullum tana watsi da zargin cewa ƙwayar cutar ta fita ne daga ɗakin kimiyya, inda take danganta hakan da haramben siyasa na Amurka.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp