fidelitybank

Amurka ta gano China ta yaɗa cutar Korona da gangan a duniya

Date:

Hukumar leƙen asiri ta Amurka, CIA, ta gabatar da sabon bayani kan binciken da ta yi game da abin da ake ganin ya haddasa annobar Korona (Covid19) a duniya, inda ta ce tana ganin zai fi yuwuwa ƙwayar cutar ta fita ne daga ɗakin bincike na kimiyya saɓanin daga jikin dabbobi.

Kakakin hukumar ya ce bisa ga dukkan alamu ɓullar cutar na da alaƙa da aikin bincike -maimakon a ce haka kawai ta ɓulla, kamar yadda rahoto ya nuna.

To amma kuma hukumar ta CIA ta ce ba ta da cikakken ƙwarin gwiwa a kan hakan.

Shawarar fitar da wannan sakamako ta kasance ɗaya daga cikin matakan da sabon shugaban hukumar ta CIA, John Ratcliffe, wanda Donald Trump ya naɗa ranar Alhamis, ya yi.

Daman tun a lokacin Trump na farko Ratcliffe, wanda a lokacin darekta ne a hukumar samar da tsaro ga shugaban ƙasa, yana da ra’ayin cewa cutar ta ɓulla ne daga ɗakin kimiyya na cibiyar binciken kimiyya ta Wuhan da ke China.

Cibiyar tana da tazarar tafiyar minti 40 ne a mota daga kasuwar da ake sayar da kifi da sauran naman ruwa – inda ake cewa daga kasuwar ne cutar ta ɓulla.

China dai a kullum tana watsi da zargin cewa ƙwayar cutar ta fita ne daga ɗakin kimiyya, inda take danganta hakan da haramben siyasa na Amurka.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Najeriya na neman dala biliyan 25 na bututun iskar gas zuwa Turai

Najeriya na neman dala biliyan 25 a matsayin kuɗin...

‘Yan sa-kai biyu ne suka mutu a harin da muka kai Zamfara – Sojoji

Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai...

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...
X whatsapp