Gwamnatin Joe Biden na Amurka na shirin bayar da gudunmuwar karin dala miliyan 308 a matsayin taimakon jin kai ga Afghanistan, wanda zai kawo jimillar taimakon da Amurka ke bayarwa ga kasar da ke fama da talauci da kuma ‘yan gudun hijirar Afghanistan da ke yankin zuwa kusan dala miliyan 782 tun daga watan Oktoba.
Fadar White House ta kara da cewa, Amurka ta na kuma samar da karin alluran rigakafin cutar coronavirus miliyan daya zuwa Afghanistan, wanda ya kawo adadin miliyan 4.3.
Taimakon da hukumar raya kasa da kasa ta Amurka za ta bayar, ta hanyar kungiyoyin jin kai masu zaman kansu, domin samar da matsuguni da kula da lafiya da taimakon sanyi da agajin abinci na gaggawa da ruwa da kuma tsaftar muhalli, in ji gwamnatin.
Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan mutane miliyan 23 na kashi 55% na al’ummar kasar Afghanisatn ke fuskantar matsananciyar yunwa, inda kusan mutane miliyan 9 ke fuskantar barazanar yunwa yayin da lokacin sanyi ke kankama.
Rikicin tattalin arzikin Afganistan ya kara tsananta, bayan da ‘yan Taliban su ka kwace mulki a watan Agusta, yayin da tsohuwar gwamnatin da kasashen Yamma ke marawa baya, sannan sojojin Amurka na karshe su ka janye.
A watan da ya gabata, Amurka a hukumance ta kebe jami’an Amurka da na Majalisar Dinkin Duniya da ke kasuwanci da ‘yan Taliban daga takunkumin Amurka, domin kokarin kiyaye kwararar kayan agaji zuwa Afganistan yayin da ta shiga cikin mawuyacin hali.