fidelitybank

Amurka ta baiwa Afghanistan tallafin kudi dala miliyan 308

Date:

Gwamnatin Joe Biden na Amurka na shirin bayar da gudunmuwar karin dala miliyan 308 a matsayin taimakon jin kai ga Afghanistan, wanda zai kawo jimillar taimakon da Amurka ke bayarwa ga kasar da ke fama da talauci da kuma ‘yan gudun hijirar Afghanistan da ke yankin zuwa kusan dala miliyan 782 tun daga watan Oktoba.

Fadar White House ta kara da cewa, Amurka ta na kuma samar da karin alluran rigakafin cutar coronavirus miliyan daya zuwa Afghanistan, wanda ya kawo adadin miliyan 4.3.

Taimakon da hukumar raya kasa da kasa ta Amurka za ta bayar, ta hanyar kungiyoyin jin kai masu zaman kansu, domin samar da matsuguni da kula da lafiya da taimakon sanyi da agajin abinci na gaggawa da ruwa da kuma tsaftar muhalli, in ji gwamnatin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan mutane miliyan 23 na kashi 55% na al’ummar kasar  Afghanisatn ke fuskantar matsananciyar yunwa, inda kusan mutane miliyan 9 ke fuskantar barazanar yunwa yayin da lokacin sanyi ke kankama.

Rikicin tattalin arzikin Afganistan ya kara tsananta, bayan da ‘yan Taliban su ka kwace mulki a watan Agusta, yayin da tsohuwar gwamnatin da kasashen Yamma ke marawa baya, sannan sojojin Amurka na karshe su ka janye.

A watan da ya gabata, Amurka a hukumance ta kebe jami’an Amurka da na Majalisar Dinkin Duniya da ke kasuwanci da ‘yan Taliban daga takunkumin Amurka, domin kokarin kiyaye kwararar kayan agaji zuwa Afganistan yayin da ta shiga cikin mawuyacin hali.

 

pulse news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp