fidelitybank

Amurka ta baiwa Afghanistan tallafin kudi dala miliyan 308

Date:

Gwamnatin Joe Biden na Amurka na shirin bayar da gudunmuwar karin dala miliyan 308 a matsayin taimakon jin kai ga Afghanistan, wanda zai kawo jimillar taimakon da Amurka ke bayarwa ga kasar da ke fama da talauci da kuma ‘yan gudun hijirar Afghanistan da ke yankin zuwa kusan dala miliyan 782 tun daga watan Oktoba.

Fadar White House ta kara da cewa, Amurka ta na kuma samar da karin alluran rigakafin cutar coronavirus miliyan daya zuwa Afghanistan, wanda ya kawo adadin miliyan 4.3.

Taimakon da hukumar raya kasa da kasa ta Amurka za ta bayar, ta hanyar kungiyoyin jin kai masu zaman kansu, domin samar da matsuguni da kula da lafiya da taimakon sanyi da agajin abinci na gaggawa da ruwa da kuma tsaftar muhalli, in ji gwamnatin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan mutane miliyan 23 na kashi 55% na al’ummar kasar  Afghanisatn ke fuskantar matsananciyar yunwa, inda kusan mutane miliyan 9 ke fuskantar barazanar yunwa yayin da lokacin sanyi ke kankama.

Rikicin tattalin arzikin Afganistan ya kara tsananta, bayan da ‘yan Taliban su ka kwace mulki a watan Agusta, yayin da tsohuwar gwamnatin da kasashen Yamma ke marawa baya, sannan sojojin Amurka na karshe su ka janye.

A watan da ya gabata, Amurka a hukumance ta kebe jami’an Amurka da na Majalisar Dinkin Duniya da ke kasuwanci da ‘yan Taliban daga takunkumin Amurka, domin kokarin kiyaye kwararar kayan agaji zuwa Afganistan yayin da ta shiga cikin mawuyacin hali.

 

hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...
X whatsapp