fidelitybank

Amurka ta baiwa Afghanistan tallafin kudi dala miliyan 308

Date:

Gwamnatin Joe Biden na Amurka na shirin bayar da gudunmuwar karin dala miliyan 308 a matsayin taimakon jin kai ga Afghanistan, wanda zai kawo jimillar taimakon da Amurka ke bayarwa ga kasar da ke fama da talauci da kuma ‘yan gudun hijirar Afghanistan da ke yankin zuwa kusan dala miliyan 782 tun daga watan Oktoba.

Fadar White House ta kara da cewa, Amurka ta na kuma samar da karin alluran rigakafin cutar coronavirus miliyan daya zuwa Afghanistan, wanda ya kawo adadin miliyan 4.3.

Taimakon da hukumar raya kasa da kasa ta Amurka za ta bayar, ta hanyar kungiyoyin jin kai masu zaman kansu, domin samar da matsuguni da kula da lafiya da taimakon sanyi da agajin abinci na gaggawa da ruwa da kuma tsaftar muhalli, in ji gwamnatin.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce kusan mutane miliyan 23 na kashi 55% na al’ummar kasar  Afghanisatn ke fuskantar matsananciyar yunwa, inda kusan mutane miliyan 9 ke fuskantar barazanar yunwa yayin da lokacin sanyi ke kankama.

Rikicin tattalin arzikin Afganistan ya kara tsananta, bayan da ‘yan Taliban su ka kwace mulki a watan Agusta, yayin da tsohuwar gwamnatin da kasashen Yamma ke marawa baya, sannan sojojin Amurka na karshe su ka janye.

A watan da ya gabata, Amurka a hukumance ta kebe jami’an Amurka da na Majalisar Dinkin Duniya da ke kasuwanci da ‘yan Taliban daga takunkumin Amurka, domin kokarin kiyaye kwararar kayan agaji zuwa Afganistan yayin da ta shiga cikin mawuyacin hali.

 

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp