Amurka ta sanar da bayar da tallafin dala miliyan 215 na gaggawa da za ta ba waiwa wasu ƙasashen Afirka da ke fuskantar ƙarancin abinci, saboda sauyin yanayi da yaƙin Ukraine da kuma annobar korona.
Sakatare Harkokin Wajen Amurka Antony Blinken ne ya bayyana hakan lokacin da ya gana da wasu ministocin Afirka a taron duniya kan abinci da Amurka ta shirya.
Amurka ta ce, tallafin zai taimaki ƙasashe wajen daƙile ƙarancin abincin.
Algeria, da Burkina Faso, da Kamaru, da Kenya, da Mauritania na cikin ƙasashen da za su amfana. Sauran su ne Najeriya, da Rwanda, da Tanzania, da Uganda, da Zimbabwe.
Ana sa ran hakan zai sauƙaƙa farashin taki da ya yi tashin gwauron-zabi tun bayan faruwar annobar korona.