Amurka na gudanar da bincike kan wasu muhimman takardu na sirri da suka fito fili, waÉ—anda ke bayyana nazarin da Amurka ke yi na shirin Isra’ila na kai wa Iran hari, kamar yadda Shugaban majalisar wakilan Amurkar Mike Johnson ya tabbatar.
Rahotanni sun ce a makon da ya wuce ne aka wallafa takardun a intanet, inda aka ce suna bayyana wasu hotunan tauraron É—an’Adam da ke nuna yadda Isra’ila ke jigilar makamai a shirin da take yi na kai harin ramuwar-gayya na harin makami mai linzami da Iran ta kai mata ranar 1 ga watan Oktoba.
Takardun waÉ—anda aka bayyana a matsayin babban sirri – Æ™asashe biyar Æ™awayen Amurka – Birtaniya da Kanada da New Zealand da kuma Australia na iya musayarsu a tsakaninsu, kamar yadda kafar yaÉ—a labarai ta CBS, da ke Amurka wadda ke alaÆ™a da BBC ra ruwaito.
Tsawon makonni Isra’ila ke duba lokaci da kuma yadda za ta kai wa Iran wannan hari – abin da ministan tsaron Isra’ilar ya yi gargaÉ—in cewa zai kasance mai muni kuma na ban mamaki da yankan shakku.
A ranar Juma’a ne aka wallafa takardun da aka danganta da hukumar nazarin bayanan sirri na kasa na Amurka da kuma hukumar tsaron kasar ta Amurka, a wani shafin sada zumunta da muhawara na Telegram da ke da alaÆ™a da Iran.
Sai dai hukumomin Amurka da Isra’ila da ke da alaka da lamarin ba su fito fili sun ce komai ba game da lamarin.
Amurka na gudanar da bincike kan ko da niyya wani jami’in leken asirinta ya fitar da takardun ko satarsu aka yi ta hanyar kutsen intanet.