fidelitybank

Amurka na ƙoƙarin cire ƙasashen da suka yi juyin mulki a Afrika daga harkokin kasuwanci

Date:

Shugaban Amurka Joe Biden, yua kaddamar da wani shiri na cire ƙasashen Uganda da Gabon da Nijar da kuma Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya daga cikin shirin bunƙasa kasuwanci na musamman tsakanin Amurka da Afirika da aka fi sani da ‘African Growth and Opportunity Act (AGOA)’.

Shugaban ya ce dalilin da ya sa aka yanke wannan shawarar shi ne, ko dai waɗannan ƙasashe sun shiga cikin jerin manyan kasashe da ke take haƙƙin ɗan’adam ko kuma ba su nuna ci gaba a mulkin dimokraɗiyya ba.

AGOA, wani shiri ne da aka ƙaddamar a cikin 2000, da ke bai wa ƙasashen Afirka na kudu da hamadar Sahara damar shiga ba Amurka ba tare da biyan haraji ba, da kayayyaki sama da 1,800.

Shugaba Biden ya ba da misali da rashin bin tsarin siyasa da bin doka da oda a matsayin dalilan rashin cancantar Nijar da Gabon, saboda juyin mulkin da sojoji suka yi a baya-bayan nan.

Ya kuma yi nuni da gagarumin take hakkin ɗan’adam da gwamnatocin kasashen Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya da Uganda suka yi a matsayin hujjar cire su daga cikin shirin.

Ya zuwa yanzu dai babu wani martani a hukumance daga ƙasashen hudu da abin ya shafa.

Wannan matakin ya biyo bayan korar da aka yi wa Burkina Faso da Mali da kuma Guinea daga AGOA bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a waɗannan kasashe.

vanguard news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp