Shugaban China Xi jinping da takwaransa na Amurka Joe Biden na daf da ganawa ta wayar tarho don tattaunawa kan yakin dake faruwa a Ukraine.
Ana kyautata zaton Shugaba Biden zai shawarci China da kar ta taimakawa Rasha da makamai. China dai batayi Allah wadai da abinda Rasha keyi ba, kuma ta zabi ta tsaya ta tsakiya ba tare da goyon bayan ko wane bangareba.
A wajen wani taron manema labarai mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen China ya yi lawadai da abin da ya kira jita jitar da ake yadawa akan rawar da China ke takawa wajen kawo karshen rikicin Ukraine.
Ya ce, China zata ci gaba da kokarin ganin an zauna domin tattaunawa sannan zata yi iya bakin kokarinta wajen warware rikicin.
Sai dai wakilin BBC a babban birnin China ya ce, gwamnatin na yada farfagandar gwamnatin Rasha game da mamayar.
Kuma China na fargabar kar takunkuman da Amurka da Turai suka kakabawa Rasha ya shafeta.