fidelitybank

Amurka da Birtaniya da Canada sun gargaɗi ‘yan kasashen su kan zanga-zangar Najeriya

Date:

Amurka da Birtaniya da Canada sun buƙaci al’ummarsu da ke zaune a Najeriya su zama masu taka-tsan-tsan inda suka yi gargaɗin yiwuwar samun tashin hankali a zanga-zangar gama-garin da ake shirin yi.

Gargaɗin ya so ne daidai lokacin da al’ummar ƙasar ke shirya zanga-zanga don nuna tura ta kai bango ga matsalolin yunwa da kuma matsin rayuwa da aka tsara somawa ranar 1 ga watan Agusta.

A wasu shawarwari da ƙasashen suka bai wa al’ummarsu da ke zaune a Najeriya, sun buƙace su da su guji wuraren da za a iya samun arangama tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar.

A na shi shawarar, ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya buƙaci Amurkawa da su nesanta kansu daga gangamin inda suka shawarce su da su kaucewa shiga dandazon jama’a su kuma ƙauracewa zanga-zanga sannan su kuma riƙa sauraron labarai.

Haka zalika, ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriyar ya yi gargaɗi cewa za a yi ganin zanga-zangar tsakanin yau 29 ga watan Yuli zuwa 10 ga watan Agusta a manyan birane kamar Abuja da Legas.

Ofishin ya buƙaci al’ummar Birtaniyar su yi kaffa-kaffa sannan su guji wuraren taron jama’a inda suka yi misali da yadda zanga-zangar da aka yi a baya ta rikiɗe zuwa tashin hankali.

Ita ma gwamnatin Canada ta shawarci al’ummarta da su bi umarnin hukumomi su kuma ci gaba da bibiyar kakafen yaɗa labarai domin sanin abin da ke wakana.

Wannan dai na nuna yadda ake nuna fargaba kan al’amura a Najeriya game da zanga-zangar da ake shirin yi da kuma tasirinta kan tsaron Najeriya.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp