fidelitybank

Amurka da Birtaniya da Canada sun gargaɗi ‘yan kasashen su kan zanga-zangar Najeriya

Date:

Amurka da Birtaniya da Canada sun buƙaci al’ummarsu da ke zaune a Najeriya su zama masu taka-tsan-tsan inda suka yi gargaɗin yiwuwar samun tashin hankali a zanga-zangar gama-garin da ake shirin yi.

Gargaɗin ya so ne daidai lokacin da al’ummar ƙasar ke shirya zanga-zanga don nuna tura ta kai bango ga matsalolin yunwa da kuma matsin rayuwa da aka tsara somawa ranar 1 ga watan Agusta.

A wasu shawarwari da ƙasashen suka bai wa al’ummarsu da ke zaune a Najeriya, sun buƙace su da su guji wuraren da za a iya samun arangama tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar.

A na shi shawarar, ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya buƙaci Amurkawa da su nesanta kansu daga gangamin inda suka shawarce su da su kaucewa shiga dandazon jama’a su kuma ƙauracewa zanga-zanga sannan su kuma riƙa sauraron labarai.

Haka zalika, ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriyar ya yi gargaɗi cewa za a yi ganin zanga-zangar tsakanin yau 29 ga watan Yuli zuwa 10 ga watan Agusta a manyan birane kamar Abuja da Legas.

Ofishin ya buƙaci al’ummar Birtaniyar su yi kaffa-kaffa sannan su guji wuraren taron jama’a inda suka yi misali da yadda zanga-zangar da aka yi a baya ta rikiɗe zuwa tashin hankali.

Ita ma gwamnatin Canada ta shawarci al’ummarta da su bi umarnin hukumomi su kuma ci gaba da bibiyar kakafen yaɗa labarai domin sanin abin da ke wakana.

Wannan dai na nuna yadda ake nuna fargaba kan al’amura a Najeriya game da zanga-zangar da ake shirin yi da kuma tasirinta kan tsaron Najeriya.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp