fidelitybank

Amurka ba ta da hannu a kisan Haniyeh – Amurka

Date:

Sakataren harkokin wajen Amurka, Antony Blinken, ya ce, ƙasarsa ba ta da masaniya ko kuma hannu a kisan da aka yi wa Isma’il Haniyeh jagoran siyasar Hamas.

Sakataren harkokin wajen Amurkan, ya ce, ba zai iya cewa ga abin da lamarin ke nufi ba, amma ya jaddada muhimmancin samun tsagaita wuta a Gaza.

Shi kuwa firaiministan Qatar, wadda ke shiga tsakani a tattaunawar tsagaita wutar da ake, ya ce, mutuwar Mr Haniyeh za ta iya kawo cikas a tattaunawar da ake.

Tuni dai Rasha da China da kuma Turkiyya suka yi alawadai da kisan da aka yi wa Ismail Haniyeh, inda shugaba Erdogan na Turkiyya ya ce, an yi hakan ne da nufin karya lagon Falasdinawa.

Kasar Iran ta ce, akwai buƙatar su yi alwadai da wannan ta’addanci da aka yi, sannan sun sanar da Isra’ila cewa, al’ummar Iran ba za ta taba bari a kashe mata bako a kasar kuma su yi shiru ba.

An kashe shugaban harkokin siyasa na ƙungiyar Hamas Ismail Haniyeh a Iran, jim kaɗan bayan ya halarci bikin rantsar da sabon shugaban ƙasar, Masoud Pezeshkian.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp