fidelitybank

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi Allah wadai da ci gaba da tsare wani fitaccen mai amfani da shafukan sada a Najeriya mai suna Ghali Isma’ila da aka fi sani da Sultan kan zargin yaɗa wani bidiyo kan ‘lafiyar’ shugaba Tinubu.

A ƙarshen makon da ya gabata ne aka kama Sultan tare da tsare shi kan zargin da Amnesty ta bayyana da maras tushe.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce kamun da hukumar DSS ta yi wa matasahin ɗan asalin jihar Kano ya saɓa wa doka.

Amnesty ta kuma zargi jami’an DSS da zuwa gidan yarin da aka tsare Sultan tare da tilasta masa ba su lambobin sirrin buɗe wayoyinsa da na shiga shafukan sada zumuntarsa (Password) ba tare da tuntuɓar lauyoyinsa ba.

Ƙungiyar ta Amnesty ta ce hakan ya saɓa wa ƴancinsa na tsare sirri da ƴancin faɗar albarkacin baki.

Amnesty ta kuma soki yadda hukumomin Najeriya ke kamawa tare da razana masu amfani da shafukan sada zumunta wajen hana su bayyana ra’ayinsu.

Daga ƙarshe ƙungiyar ta yi kira ga hukumomin na Najeriya su gaggauta sakin matashin ba tare da wasu sharuɗɗa ba.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp