fidelitybank

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International ta yi Allah wadai da ci gaba da tsare wani fitaccen mai amfani da shafukan sada a Najeriya mai suna Ghali Isma’ila da aka fi sani da Sultan kan zargin yaɗa wani bidiyo kan ‘lafiyar’ shugaba Tinubu.

A ƙarshen makon da ya gabata ne aka kama Sultan tare da tsare shi kan zargin da Amnesty ta bayyana da maras tushe.

Cikin wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar ta ce kamun da hukumar DSS ta yi wa matasahin ɗan asalin jihar Kano ya saɓa wa doka.

Amnesty ta kuma zargi jami’an DSS da zuwa gidan yarin da aka tsare Sultan tare da tilasta masa ba su lambobin sirrin buɗe wayoyinsa da na shiga shafukan sada zumuntarsa (Password) ba tare da tuntuɓar lauyoyinsa ba.

Ƙungiyar ta Amnesty ta ce hakan ya saɓa wa ƴancinsa na tsare sirri da ƴancin faɗar albarkacin baki.

Amnesty ta kuma soki yadda hukumomin Najeriya ke kamawa tare da razana masu amfani da shafukan sada zumunta wajen hana su bayyana ra’ayinsu.

Daga ƙarshe ƙungiyar ta yi kira ga hukumomin na Najeriya su gaggauta sakin matashin ba tare da wasu sharuɗɗa ba.

www.nigeriannewspapers.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...
X whatsapp