fidelitybank

AMNESTY ta tirsasawa Tinubu ya saki Yaran da aka kama yayin zanga-zanga

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’Adam ta Amnesty International ta ce, dole ne shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar tsadar rayuwa.

Da yake martani kan batun komawa shari’ar masu zanga-zangar da aka yi a wata babbar kotun tarayya jiya a Abuja, darektan ƙungiyar a Najeriya Isa Sanusi, ya ce dole ne shugaban ƙasar ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar kuma ba tare da wani sharaɗi ba.

Ya ce tsare mutanen tun watan Agusta saboda kawai sun yi amfani da dama da ‘yancinsu na zanga-zangar lumana tare da tuhumarsu da laifuka na ban mamaki da suka haɗa da cin amanar ƙasa da ta’addanci ya nuna yadda gwamnatin Najeriya ba ta mutunta ‘yancin ɗan’Adam.

Darektan ya ce masu zanga-zangar 114 da aka gurfanar a kotun ba su yi wani abu da ya saɓa doka ba, kuma ba su cancanci irin muzgunawar da aka yi musu ba tun daga lokacin da aka kama su

Ya ce daga cikin mutum 76 da aka fara gabatarwa a kotun a jiya, yawancinsu yara ne, kuma faɗuwar hudu daga cikinsu a kotu alama ce da ta nuna mummunan yanayin da lafiyarsu ke ciki.

Shugaban ƙungiyar ta Amnesty ya ce tsare yara a irin wannan yanayi na tashin hankali a kan ƙin amincewarsu tare da neman mulki na gari ya nuna kudurin gwamnati na murƙushe masu suka.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp