fidelitybank

AMNESTY ta tirsasawa Tinubu ya saki Yaran da aka kama yayin zanga-zanga

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan’Adam ta Amnesty International ta ce, dole ne shugaban kasar Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar tsadar rayuwa.

Da yake martani kan batun komawa shari’ar masu zanga-zangar da aka yi a wata babbar kotun tarayya jiya a Abuja, darektan ƙungiyar a Najeriya Isa Sanusi, ya ce dole ne shugaban ƙasar ya saki dukkanin waɗanda aka kama a kan zanga-zangar kuma ba tare da wani sharaɗi ba.

Ya ce tsare mutanen tun watan Agusta saboda kawai sun yi amfani da dama da ‘yancinsu na zanga-zangar lumana tare da tuhumarsu da laifuka na ban mamaki da suka haɗa da cin amanar ƙasa da ta’addanci ya nuna yadda gwamnatin Najeriya ba ta mutunta ‘yancin ɗan’Adam.

Darektan ya ce masu zanga-zangar 114 da aka gurfanar a kotun ba su yi wani abu da ya saɓa doka ba, kuma ba su cancanci irin muzgunawar da aka yi musu ba tun daga lokacin da aka kama su

Ya ce daga cikin mutum 76 da aka fara gabatarwa a kotun a jiya, yawancinsu yara ne, kuma faɗuwar hudu daga cikinsu a kotu alama ce da ta nuna mummunan yanayin da lafiyarsu ke ciki.

Shugaban ƙungiyar ta Amnesty ya ce tsare yara a irin wannan yanayi na tashin hankali a kan ƙin amincewarsu tare da neman mulki na gari ya nuna kudurin gwamnati na murƙushe masu suka.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp