fidelitybank

Amnesty ta ja kunnen gwamnati kan kama shugaban ƙungiyar ƙwadago

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil’adama ta Amnesty International a Najeriya, ta nuna damuwa kan sabbin zarge-zargen taimaka wa ta’addanci da hukumomin Najeriya ke yi kan ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya NLC da shugabanninta.

A cikin wata takardar sanarwa da ta fitar, Amnesty ta soki yunkurin hukumomin gwamnati da cewa matakin da rundunar ƴansandan Najeriya ta ɗauka na gayyatar Joe Ajaero wani yunƙuri ne kawai na tursasa wa NLC ta yi abin da gwamnati ke so.

A ranar Talata ne wata sanarwa da rundunar ƴansanda ta Najeriya ta fitar ta buƙaci shugaban na NLC, Joe Ajaero ya bayyana a gabanta domin amsa tambayoyi kan wasu tuhume-tuhume da ake masa da suka shafi tallafa wa yunƙurin tayar da rikici a Najeriya.

Hakan na zuwa ne bayan wani samame da jami’an tsaro suka kai a hedikwatar ƙungiyar ta NLC, inda suka ce sun yi hakan ne a wani ɓangare na binciken da suke gudanarwa kan wani mai shirya tarzoma.

Amnesty International ta buƙaci hukumomin da su mutunta ƴancin ƙungiyoyin ƙwadago domin bayyana ra’ayoyinsu, ya kuma yi gargaɗin a guji amfani da ikon gwamnati wajen rufe bakin kungiyar ta NLC.

Amnesty International ta bayyana yadda ake samun karuwar cin zarafin ƙungiyar ƙwadagon a cikin shekarar da ta gabata, ciki har da harin da ƴansanda suka kai wa Ajaero a watan Nuwamba da wani samame da aka kai hedikwatar ta NLC a baya-bayan nan.

Kungiyar ta yi Allah-wadai da waɗannan ayyuka a matsayin katsalandan ga ƴancin kai na ƙungiyar ƙwadagon.

Amnesty ta kuma yi kira da a gaggauta kawo ƙarshen neman murƙushe shugabannin ƙungiyar ta NLC, tare da bayyana zargin da ake yi musu a matsayin maras tushe.

vanguard news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp