fidelitybank

AMNESTY ta gaggauta janye kalaman ta a kan mu ko mu dauki mataki – Rundunar ‘Yansanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan kasar nan, ta buƙaci Kungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International a Najeriya, da ta gaggauta janye kalaman da ta wallafa na zargin jami’an tsaro da aikata laifukan cin zarafin masu zanga-zanga,

Ta kuma buƙaci ƙungiyar ta nemi afuwar al’umma.

A cewar kakakin rundunar Muyiwa Adejobi, ya ce an riga an aike wa ƙungiyar wasikar tun a ranar shida ga wannan watan na Janairu, kuma muddin ba ta aiwatar da wannan buƙata ba, rundunar ƴan sandan za ta ɗauki matakin shari’a

Bayanin da rundunar ta fitar ya nuna cewa akwai abubuwa da dama da suka haɗa zarge-zargen da rundunar ƴan sandan ta ce na ƙarya ne, masu nasaba da take hakkin ɗan Adam ta hanyar azabtar da masu zanga-zanga.

Bayanin ya ce akwai hujjoji ƙarara da suka nuna babu wani abu makamancin haka da ya wanzu, ciki kuwa har da hotunan bidiyo da gidajen talabijin suka watsa kai tsaye a lokacin da ake gudanar da zanga-zangar ta watan Agustan shekarar 2024, kuma rundunar ƴan sandan ta yi nazarin ƙwaƙwaf tare da gudanar da bincike inda ta gano dukan abubuwan da kungiyar ta yi iƙirari ba su da ƙamshin gaskiya.

A cewar rundunar ƴansandar Najeriyar, jami’anta sun yi amfani da ƙwarewa tare da bin cikakkun ka’idojin aikin da aka san jami’an tsaro da su, har ma a wuraren da suka fuskanci farmaki daga masu zanga-zanga bai sa sun yi amfani da ƙarfin da ya wuce kima ba.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp