Rundunar ‘yan sandan kasar nan, ta buƙaci Kungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International a Najeriya, da ta gaggauta janye kalaman da ta wallafa na zargin jami’an tsaro da aikata laifukan cin zarafin masu zanga-zanga,
Ta kuma buƙaci ƙungiyar ta nemi afuwar al’umma.
A cewar kakakin rundunar Muyiwa Adejobi, ya ce an riga an aike wa ƙungiyar wasikar tun a ranar shida ga wannan watan na Janairu, kuma muddin ba ta aiwatar da wannan buƙata ba, rundunar ƴan sandan za ta ɗauki matakin shari’a
Bayanin da rundunar ta fitar ya nuna cewa akwai abubuwa da dama da suka haɗa zarge-zargen da rundunar ƴan sandan ta ce na ƙarya ne, masu nasaba da take hakkin ɗan Adam ta hanyar azabtar da masu zanga-zanga.
Bayanin ya ce akwai hujjoji ƙarara da suka nuna babu wani abu makamancin haka da ya wanzu, ciki kuwa har da hotunan bidiyo da gidajen talabijin suka watsa kai tsaye a lokacin da ake gudanar da zanga-zangar ta watan Agustan shekarar 2024, kuma rundunar ƴan sandan ta yi nazarin ƙwaƙwaf tare da gudanar da bincike inda ta gano dukan abubuwan da kungiyar ta yi iƙirari ba su da ƙamshin gaskiya.
A cewar rundunar ƴansandar Najeriyar, jami’anta sun yi amfani da ƙwarewa tare da bin cikakkun ka’idojin aikin da aka san jami’an tsaro da su, har ma a wuraren da suka fuskanci farmaki daga masu zanga-zanga bai sa sun yi amfani da ƙarfin da ya wuce kima ba.