fidelitybank

Amnesty ta buƙaci gwamnan Kano ya kafa kwamiti kan binciken kisan ƴan Zanga-zanga

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil-adama ta Amnesty International ta yi kira ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gaggauta kafa kwamitin shari’a mai zaman kanta domin binciken kisan da ƙungiyar ta bayyana da na ”ganganci” kan aƙalla masu zanga-zanga 10 a unguwannin Kurna da Kofar Nasarawa.

Cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Isa Sanusi ya fitar, ya ce dole ne kwamitin ya yi aikinsa, ba tare da katsalandan ba, kuma ya zama wajibi gwamnati ta ba shi duk abin da yake buƙata don gudanar da aikinsa.

Ƙungiyar ta kuma ce dole ne a binciki yadda jami’an tsaron Najeriya suka tinkari zanga-zangar, da kuma irin ɓarnar da ”yan dabar” da aka yi zargin hayarsu domin kawo fitina a lokacin zanga-zangar.

“Rashin gudanar da bincike kan kashe-kashe da lalata dukiyoyi da aka yi a Kano tun daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa yau, ka iya kawo tarnaƙi ga bin doka da Oda”

Sanarwa ta ƙara da cewa rashin binciken zai sa ɗabi’ar nan ta rashin hukunta masu laifi ta ci gaba da wanzuwa a ƙasar, kamar yadda dama ba sabon abu ba ne a Najeriya, in ji sanarwar.

An dai samu hatsaniya a lokacin zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da aka gudanar a Kano cikin makon nan, inda aka zargi jami’an tsaro da harbe masu zanga-zangar.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...
X whatsapp