fidelitybank

Amnesty ta buƙaci gwamnan Kano ya kafa kwamiti kan binciken kisan ƴan Zanga-zanga

Date:

Ƙungiyar kare haƙƙin bil-adama ta Amnesty International ta yi kira ga gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya gaggauta kafa kwamitin shari’a mai zaman kanta domin binciken kisan da ƙungiyar ta bayyana da na ”ganganci” kan aƙalla masu zanga-zanga 10 a unguwannin Kurna da Kofar Nasarawa.

Cikin wata sanarwa da daraktan ƙungiyar, Isa Sanusi ya fitar, ya ce dole ne kwamitin ya yi aikinsa, ba tare da katsalandan ba, kuma ya zama wajibi gwamnati ta ba shi duk abin da yake buƙata don gudanar da aikinsa.

Ƙungiyar ta kuma ce dole ne a binciki yadda jami’an tsaron Najeriya suka tinkari zanga-zangar, da kuma irin ɓarnar da ”yan dabar” da aka yi zargin hayarsu domin kawo fitina a lokacin zanga-zangar.

“Rashin gudanar da bincike kan kashe-kashe da lalata dukiyoyi da aka yi a Kano tun daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa yau, ka iya kawo tarnaƙi ga bin doka da Oda”

Sanarwa ta ƙara da cewa rashin binciken zai sa ɗabi’ar nan ta rashin hukunta masu laifi ta ci gaba da wanzuwa a ƙasar, kamar yadda dama ba sabon abu ba ne a Najeriya, in ji sanarwar.

An dai samu hatsaniya a lokacin zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da aka gudanar a Kano cikin makon nan, inda aka zargi jami’an tsaro da harbe masu zanga-zangar.

naija news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp