fidelitybank

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Date:

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da ta ce, gwamnatin Najeriya na yi kan ɓacewar matashin ɗan gwagwarmaya, Abubakar Idris Dadiyata.

Amnesty International ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da ta raba wa manema labarai, inda ta ce tana mamakin yadda aka yi shekara shida ba tare da sanin halin da yake ciki ba.

Dadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan shekarar 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun kutsa gidansa da ke unguwar Barnawa a Kaduna jim kaɗan bayan ya koma, suka suka tafi da shi.

“Tun lokacin ne iyalansa suke ta da jiran komawarsa, amma har yanzu da ya cika shekara shida babu bayani.”

Shugaban ƙungiyar a Najeriya, Isa Sanusi ya ce shi kansa ya san Dadiyata a matsayin jajirtacce mai girmama na gaba.

“Amnesty ta yi amannar cewa ɓacewar Dadiyata na da nasaba da sukar gwamnati da wasu ƴansiyasa a kafofin sadarwa da yake yi ba.”

Amnesty ta ce duk da gwamnati ta ce ba ta da hannu a ɓacewarsa, “duk da haka dole a zargi gwamnati. Kuma bayan haka, haƙƙin gwamnati ne ta rufe duk wasu ƙoƙofin zargi game da ɓacewar matashin ta hanyar ganowa da bayyana asalin abin da ya faru da Dadiyata domin sauƙaƙa ƙuncin da iyalansa da ƴanuwansa da abokan arziki suke ciki.

Amnesty ta ce akwai buƙatar jami’an tsaron Najeriya su ƙara ƙaimi wajen bincike domin gano asalin abin da ya faru, tare da bayyana abin da suka gano, “abin mamaki ne a ce shekara shida an kasa samu tabbataccen bayani. Tilas shugaban Najeriya Bola Tinubu ya sa baki a kan batun ɓacewar Dadiyata.”

“Don haka muna Allah-wadai da rashin kula da gwamnatin Najeriya take ba batun ɓacewar Dadiyata, kuma lokaci na ƙara ƙurewa. Ƴan’uwa da iyalan Dadiyata na neman amsar tambayar: ina Dadiyata yake?”

Daga cikin waɗanda suka halarci taron akwai matarsa, Khadija Lame da ƙaninsar Usman Idris.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...
X whatsapp