fidelitybank

Ambaliyar ruwan sama a Jigawa ya kashe mutane 25

Date:

Hukumar agajin gaggawa ta jihar Jigawa, ta ce, ambaliyar ruwan da mamakon ruwan saman da ake a sassan jihar ya haddasa, ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum 25.

Babban darakta a hukumar, Dakta Haruna Mai Riga, ya shaida wa BBC cewa, a kullum adadin waɗanda ke mutuwa sakamakon ambaliyar ruwan na ƙaruwa saboda mamakon ruwan saman da ake na janyo gidaje na ruftawa wani lokacin a kan mutane.

Ya ce, baya ga asarar rai, ambaliyar ruwan ta lalata gonaki da faɗinsu ya kai hecta 3,926 a sassa daban-daban na jihar.

Dakta Mai Riga, ya ce,” Ambaliyar ruwan ta sa mutane 17,732, sun rasa muhallansu a ƙanana hukumomin da suka haɗar da Auyo da Buji da Gwaram da Garki da Kirika Samma da Maigatari da Kafin Hausa da Malam Madori da Haɗeja da Kiyawa da kuma Jahun.”

Shugaban hukumar ya ce a yanzu hukumarsu da kuma gwamnatin jihar na ƙokari wajen taimakawa waɗanda ambaliyar ta shafa, inda ya ce,” Mun kai kayan agaji wasu yankunan kamar katifa da gidan sauro da kuma kayan abinci.”

Ya ce, a yanzu an tsugunnar da waɗanda ambaliyar ta shafewa ko rusa wa gidaje a makarantun dake garuruwan.

Dakta Mai Riga, ya ce jama’a su kwantar da hankulansu, hukumarsu dama gwamnatin jihar tana sane da halin da jama’a ke ciki.

Ba wannan ne karon farko da ambaliyar ta afkawa jihar Jigawa ba, inda ko a 2020, jihar ta fuskanci mummunan ambaliyar da ta janyo asarar rayuka da kuma dukiya mai yawa.

leadership newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp