Ambaliyar ruwa ta lalata gidaje da kadada na gonaki a karamar hukumar Buji ta jihar Jigawa.
Hakimin Gantsa dake Buji Alh. Sabo ya bayyana haka ne a lokacin da tawagar hukumar bada agajin gaggawa ta kasa (NEMA) ta ma’aikatar muhalli ta jihar Jigawa ta ziyarci wasu kauyukan da ambaliyar ruwa ta shafa.
A cewarsa “Kwanaki uku kenan ko’ina ya cika ruwa, ruwan yana fitowa daga wasu sassan jihar Bauch, musamman Itasgadau, yana zuwa ta cikin kananan kwari.
“Dukan noman shinkafa da masara sun yi ambaliya a halin yanzu, ba mu san takamaiman kiyasin gonaki da gidajen da aka lalata ba.
“Haka nan a garin Gantsa, gidaje da dama sun nutse kuma yanzu haka suna tare da ‘yan uwansu,” in ji shi.
Ya bukaci ma’aikatar muhalli da ta gina katanga a kewayen yankin domin hana afkuwar lamarin.
Shima da yake jawabi, Dr Haruna Mairiga, babban sakataren hukumar SEMA a jihar, ya jajantawa wadanda abin ya shafa.
Ya ce tuni gwamnan ya umurci hukumar ta gudanar da tantance barnar da aka yi domin a taimaka wa wadanda abin ya shafa.