fidelitybank

Ambaliyar ruwa ya raba yara miliyan 2.2 daga muhallin su da makaranta a Najeriya – UNICEF

Date:

Asusun Tallafawa Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF, ya bayyana cewa ambaliyar ruwa a shekarar 2024 ta raba kimanin dalibai miliyan 2.2 da muhallansu a fadin Najeriya, lamarin da ke kawo cikas ga harkokin ilimi a fadin kasar.

Shugabar ofishin UNICEF na Kano, Rahama Farah, ce ta bayyana hakan a yayin taron manema labarai na bikin ranar ilimi ta duniya ta 2025 (IDE).

A wani rahoto da UNICEF ta fitar, an ce gaba daya dalibai miliyan 2,200,200 ne bala’in ambaliyar ruwa ya shafa kai tsaye, lamarin da ya kai ga rufe makarantu da kuma katse karatun miliyoyin yara.

“A jihar Jigawa kadai, ambaliyar ruwan da ta faru a shekarar da ta gabata ta lalata gine-ginen makarantu 115, abin da ya sa ba su da aminci don amfani da su tare da kawo cikas ga harkokin ilimi,” in ji Mista Farah.

Ya kara da cewa, sama da yara ‘yan makaranta 92,518—wanda ya kunshi mata 43,813 da maza 48,705—an fama da matsalar a dukkanin kananan hukumomin jihar Jigawa 27.

Lallacewar ababen more rayuwa da kuma tsawaita rufewa sun hana É—alibai samun mahimman damar koyo.

Domin magance illar sauyin yanayi ga ilimi, UNICEF tare da hadin gwiwar ofishin kula da harkokin kasashen waje, Commonwealth, da kuma ci gaban kasa (FCDO) na kasar Birtaniya, suna tallafa wa gwamnatocin jihohin Kano da Jigawa don samar da yanayin koyo.

“UNICEF ta dauki matasa 1,000 – 350 a Jigawa da 650 a Katsina – don dasa itatuwa 300 a cikin hamada da wuraren da ake fama da ambaliyar ruwa a cikin jihohin biyu a wani mataki na yaki da sauyin yanayi,” Mista Farah ya bayyana.

Bugu da kari, UNICEF ta gina wuraren samar da ruwa, tsaftar muhalli, da tsafta (WASH) masu jure yanayi a makarantu da dakunan shan magani a yankunan da kalubalen yanayi ya fi shafa a jihohin uku.

Mista Farah ya jaddada ci gaba da jajircewar UNICEF wajen rage tasirin sauyin yanayi kan ilimi da tabbatar da aminci, dauwamammen yanayin koyo ga yara.

news today in nigeria 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan ÆŠaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp