fidelitybank

Ambaliyar ruwa ya kashe mutane bakwai a Bauchi

Date:

Hukumomi a ƙaramar hukumar Shira ta jihar Bauchi, sun tabbatar da mutuwar mutum bakwai sanadiyar ambaliyar da aka samu sakamakon mamakon ruwan sama.

Hukumomi a ƙaramar hukumar sun ce mamakon ruwan sama da aka shafe sa’oi ana yi a ƙarshen mako ne ya janyo ambaliyar ruwan.

Kantoman ƙaramar hukumar Babangida Ishaq Maliya, ya shaida wa BBC cewa, ruwan saman da aka yi ya yi sanadin rushewar gidaje da dama ga shafe gonaki, sannan kuma akwai waɗanda ma gini ya rufta musu.

Ya ce akwai ‘yar shekara 80 da ginin ma ya rufta mata, da ‘yar shekara 15 da kuma yaro wanda ta ke suka mutu.

“Baya ga waɗannan mutum ukun, akwai garin Dango, wanda anan ma mace ɗaya ‘yar shekara 15 da mutu, sai garin ƙaura da namiji guda ya mutu sai kuma garin Kungu da anan ma mace guda ta rasu.

Mazauna ƙauyen Sunkuye, wato ɗaya daga cikin ƙauyukan da aka samu ambaliyar sun ce har ruwa ya tafi da wani yaro da har kawo yanzu ba a ganshi ba.

Mutanen garin sun ce yanzu suna cikin jimami da tararrabin abin da zai iya faruwa da su saboda tsabar ruwan saman da ake kamar da bakin ƙwarya.

A ɓangaren gwamnatin jihar, babban darakta a hukumar agajin gaggawa ta jihar, Mas’udu Aliyu, ya shaida wa BBC cewa, ambaliyar ruwan ta fi muni a ƙananan hukumomi uku,wato Shira da Katagun da kuma Giade.

Ya ce tuni gwamnan jihar ya kafa kwamiti don bayar da agaji ga waɗanda ambaliyar ta shafa.

Rahotanni sun ce ambaliyar ta yi sanadin lalacewar hanyoyin da dama a arewacin Najeriya ciki har da Bauchi da Jigawa, inda babbar hanyar data haɗa Bauchi da Kano ta karye al’amarin da ya sa sai da ƙyar da dabara motoci ke wucewa.

legits news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp