Hukumomi a ƙaramar hukumar Shira ta jihar Bauchi, sun tabbatar da mutuwar mutum bakwai sanadiyar ambaliyar da aka samu sakamakon mamakon ruwan sama.
Hukumomi a ƙaramar hukumar sun ce mamakon ruwan sama da aka shafe sa’oi ana yi a ƙarshen mako ne ya janyo ambaliyar ruwan.
Kantoman ƙaramar hukumar Babangida Ishaq Maliya, ya shaida wa BBC cewa, ruwan saman da aka yi ya yi sanadin rushewar gidaje da dama ga shafe gonaki, sannan kuma akwai waɗanda ma gini ya rufta musu.
Ya ce akwai ‘yar shekara 80 da ginin ma ya rufta mata, da ‘yar shekara 15 da kuma yaro wanda ta ke suka mutu.
“Baya ga waɗannan mutum ukun, akwai garin Dango, wanda anan ma mace ɗaya ‘yar shekara 15 da mutu, sai garin ƙaura da namiji guda ya mutu sai kuma garin Kungu da anan ma mace guda ta rasu.
Mazauna ƙauyen Sunkuye, wato ɗaya daga cikin ƙauyukan da aka samu ambaliyar sun ce har ruwa ya tafi da wani yaro da har kawo yanzu ba a ganshi ba.
Mutanen garin sun ce yanzu suna cikin jimami da tararrabin abin da zai iya faruwa da su saboda tsabar ruwan saman da ake kamar da bakin ƙwarya.
A ɓangaren gwamnatin jihar, babban darakta a hukumar agajin gaggawa ta jihar, Mas’udu Aliyu, ya shaida wa BBC cewa, ambaliyar ruwan ta fi muni a ƙananan hukumomi uku,wato Shira da Katagun da kuma Giade.
Ya ce tuni gwamnan jihar ya kafa kwamiti don bayar da agaji ga waɗanda ambaliyar ta shafa.
Rahotanni sun ce ambaliyar ta yi sanadin lalacewar hanyoyin da dama a arewacin Najeriya ciki har da Bauchi da Jigawa, inda babbar hanyar data haɗa Bauchi da Kano ta karye al’amarin da ya sa sai da ƙyar da dabara motoci ke wucewa.