Hukumomi a jihar Filato sun ce, gomman gidaje ne suka rushe sanadin ambaliyar ruwa a wasu sassan jihar, lamarin da ya shafi ɗaruruwan magidanta. Ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya a ranar Laraba ne ya haddasa ambaliyar ta yi wannan gagarumar ɓarna.
Daya daga cikin wadanda ambaliyar ta shafa a Jos babban birnin jihar Filato, yace awa hudu aka kwashe ana tafka ruwan saman, kuma ya yi sanadin rushewar gomman gidaje da lalata dukiya, Mutumin ya ce yawancin wadanda ambaliyar ta shafa, sun samu mafaka ne a gidajen ‘yan uwa da abokan arziki.
Mukaddashin sakataren hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Fitalo Mista Chuwang, ya ce gidaje sun ruguje, dukiya ta salwanta, ruwan ya yi awon gaba da kaya, mutane na cikin halin rashin tabbas da neman agaji.
A jihar Neja ma, hukumomi na can suna kokarin tantance barnar da ambaliyar ruwan sama ta yi musamman a yankin Kwantagora. In ji BBC.
Hukumomin jihar sun dukufa don kididdige yawan asarar da aka samu sanadiyar ambaliyar ruwan a Kwantagora. Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa na jihar Ahmad Ibrahim Inga, yace za su kara tura tawaga ta musamman da kayan aiki don tallafawa mutanen da ambaliyar ta shafa.
Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin cewa wasu jihohi za su fuskanci ruwan sama kamar da bakin kwarya na tsawon kwanaki hudu daga ranar Laraba har zuwa Asabar.
Sannan tun kafin shi din ma, anata kokawa da karuwar ruwan saman da manazarta ke cewa a wasu lokutan ake shafe tsawon kwana ko wuni guda ana yi.