fidelitybank

Ambaliyar ruwa ta rushe gidaje a Filato da Neja

Date:

Hukumomi a jihar Filato sun ce, gomman gidaje ne suka rushe sanadin ambaliyar ruwa a wasu sassan jihar, lamarin da ya shafi ɗaruruwan magidanta. Ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya a ranar Laraba ne ya haddasa ambaliyar ta yi wannan gagarumar ɓarna.

Daya daga cikin wadanda ambaliyar ta shafa a Jos babban birnin jihar Filato, yace awa hudu aka kwashe ana tafka ruwan saman, kuma ya yi sanadin rushewar gomman gidaje da lalata dukiya, Mutumin ya ce yawancin wadanda ambaliyar ta shafa, sun samu mafaka ne a gidajen ‘yan uwa da abokan arziki.

Mukaddashin sakataren hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Fitalo Mista Chuwang, ya ce gidaje sun ruguje, dukiya ta salwanta, ruwan ya yi awon gaba da kaya, mutane na cikin halin rashin tabbas da neman agaji.

A jihar Neja ma, hukumomi na can suna kokarin tantance barnar da ambaliyar ruwan sama ta yi musamman a yankin Kwantagora. In ji BBC.

Hukumomin jihar sun dukufa don kididdige yawan asarar da aka samu sanadiyar ambaliyar ruwan a Kwantagora. Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa na jihar Ahmad Ibrahim Inga, yace za su kara tura tawaga ta musamman da kayan aiki don tallafawa mutanen da ambaliyar ta shafa.

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin cewa wasu jihohi za su fuskanci ruwan sama kamar da bakin kwarya na tsawon kwanaki hudu daga ranar Laraba har zuwa Asabar.

Sannan tun kafin shi din ma, anata kokawa da karuwar ruwan saman da manazarta ke cewa a wasu lokutan ake shafe tsawon kwana ko wuni guda ana yi.

the sun newspaper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp