fidelitybank

Ambaliyar ruwa ta rushe gidaje a Filato da Neja

Date:

Hukumomi a jihar Filato sun ce, gomman gidaje ne suka rushe sanadin ambaliyar ruwa a wasu sassan jihar, lamarin da ya shafi ɗaruruwan magidanta. Ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya a ranar Laraba ne ya haddasa ambaliyar ta yi wannan gagarumar ɓarna.

Daya daga cikin wadanda ambaliyar ta shafa a Jos babban birnin jihar Filato, yace awa hudu aka kwashe ana tafka ruwan saman, kuma ya yi sanadin rushewar gomman gidaje da lalata dukiya, Mutumin ya ce yawancin wadanda ambaliyar ta shafa, sun samu mafaka ne a gidajen ‘yan uwa da abokan arziki.

Mukaddashin sakataren hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Fitalo Mista Chuwang, ya ce gidaje sun ruguje, dukiya ta salwanta, ruwan ya yi awon gaba da kaya, mutane na cikin halin rashin tabbas da neman agaji.

A jihar Neja ma, hukumomi na can suna kokarin tantance barnar da ambaliyar ruwan sama ta yi musamman a yankin Kwantagora. In ji BBC.

Hukumomin jihar sun dukufa don kididdige yawan asarar da aka samu sanadiyar ambaliyar ruwan a Kwantagora. Shugaban hukumar ba da agajin gaggawa na jihar Ahmad Ibrahim Inga, yace za su kara tura tawaga ta musamman da kayan aiki don tallafawa mutanen da ambaliyar ta shafa.

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya ta yi gargadin cewa wasu jihohi za su fuskanci ruwan sama kamar da bakin kwarya na tsawon kwanaki hudu daga ranar Laraba har zuwa Asabar.

Sannan tun kafin shi din ma, anata kokawa da karuwar ruwan saman da manazarta ke cewa a wasu lokutan ake shafe tsawon kwana ko wuni guda ana yi.

sun news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp