fidelitybank

Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 11 a jihar Neja

Date:

Mummunar ambaliya ruwa ta yi sanadin mutuwar mutum 11 a jihar Neja da ke tsakiyar Najeriya, tare da lalata garuruwa masu yawa faɗin ƙananan hukumomi 19 daga cikin 25 da ke jihar.

Cikin wata sanarwa da daraktan hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar, Abdullahi Baba-Arah, ya fitar ya ce lamarin ya lalata gidaje fiye da 6,865, tare da gonaki 118,692, kamar yadda gidan talbijin na Channels ya ruwaito.

Lamarin ya jefa fiye da mutum 41,000 cikin tsananin buƙatar tallafi.

Baya ga lalata gonakin, ambaliyar ta kuma shafi makarantu 246, lamarin da ya shafi harkokin ilimi a garuruwa 529 na jihar.

Ƙananan hukumomin da lamarin ya fi ƙamari sun haɗa da Mokwa da Katcha da Lavun da Lapai da Agaie da Shiroro da Munya da Gbako da Kontagora da Bosso da Edati da Agwara da Bida da Magama da Mashegu da Borgu da Gurara da Suleja da ƙaramar hukumar Rijau.

Rahotonni sun ce ambaliyar ta kuma shafi gadoji 18 da kwalbatoci 80, lamarin da ya kawo cikas ga harkokin sufuri a wasu yankunan jihar.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp