fidelitybank

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Date:

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da wuraren ibada a jihohin Bauchi da Filato da kuma jihar Neja, lamarin da ya tilasta wa ɗaruruwan mutane barin gidajensu.

Mazauna yankunan da lamarin ya faru sun ce ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya haɗe da iska a wayewar garin ranar Lahadi, ya kayar da bishiyoyi tare da tsige turakun lantarki da ɗaye kwanukan rufi lamarin da ya sa gine-gine da dama suka faɗi.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa fiye da gine-gine 50 ne suka rushe sakamakon ambaliyar a garin Menkaat na ƙaramar hukumar Shendam a jihar filato.

Can a ƙaramar hukumar Dass ta jihar Bauchi fiye da magidanta 40 suka rasa muhallansu sakamakon ambaliyar da ta lalata gonaki masu yawa a cewar Jaridar.

Haka a jihar Neja kusan garuruwa 18 ne suka fuskanci ambaliyar a ƙaramar hukumar Lapai ta jihar Neja, inda ruwa ya cinye gonaki masu yawa.

Lamarin na zuwa ne dai a daidai lokacin da hukumar hasashen yanayi ta ƙasar, (Nimet) ke gargaɗin samun ruwan sama haɗe da tsawa da yiwuwar samun ambaliya a wasu jihohin ƙasar.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin Isra’ila sun kashe Falasdinawa wajen karbar abinci

Rahotanni daga Gaza na cewa sojojin Isra'ila sun sake...

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da...

Najeriya ta lashe gasar kwallon kwandon Afrika

Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe...

Obi ba zai iya lashe zabe a yankin Arewa ba – Keyamo

Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya ce ɗaya...

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...
X whatsapp