fidelitybank

Ambaliya ya shanye jihohin Bauchi da Filato da kuma Neja

Date:

Ambaliya ta cinye gonaki da gidaje da makarantu da wuraren ibada a jihohin Bauchi da Filato da kuma jihar Neja, lamarin da ya tilasta wa ɗaruruwan mutane barin gidajensu.

Mazauna yankunan da lamarin ya faru sun ce ruwan saman da aka samu kamar da bakin ƙwarya haɗe da iska a wayewar garin ranar Lahadi, ya kayar da bishiyoyi tare da tsige turakun lantarki da ɗaye kwanukan rufi lamarin da ya sa gine-gine da dama suka faɗi.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito cewa fiye da gine-gine 50 ne suka rushe sakamakon ambaliyar a garin Menkaat na ƙaramar hukumar Shendam a jihar filato.

Can a ƙaramar hukumar Dass ta jihar Bauchi fiye da magidanta 40 suka rasa muhallansu sakamakon ambaliyar da ta lalata gonaki masu yawa a cewar Jaridar.

Haka a jihar Neja kusan garuruwa 18 ne suka fuskanci ambaliyar a ƙaramar hukumar Lapai ta jihar Neja, inda ruwa ya cinye gonaki masu yawa.

Lamarin na zuwa ne dai a daidai lokacin da hukumar hasashen yanayi ta ƙasar, (Nimet) ke gargaɗin samun ruwan sama haɗe da tsawa da yiwuwar samun ambaliya a wasu jihohin ƙasar.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp