Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon wata mummunar ambaliya da ta afku a garin Mokwa, hedikwatar karamar hukumar Mokwa da ke jihar Neja.
Mazauna yankin sun bayyana cewa ambaliyar ta katse hanyar da ke hade Arewa da Kudancin Najeriya ta hanyar Mokwa, lamarin da ya jefa matafiya cikin kunci.
Kodayake cikakken bayani bai fito ba tukuna, wasu mazauna yankin sun ce kimanin mutane 50 ne suka rasa rayukansu a musibar.
Har yanzu ana neman wasu mazauna yankin ciki har da mata da ƙananan yara da suka bace. An kuma ruwaito cewa gidaje da dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira sun nutse sakamakon ambaliyar.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ambaliyar ta samo asali ne daga ruwan sama mai ƙarfi da aka yi tsawon sa’o’i da dama a daren Laraba, wanda ya yi sanadin nutsewar gidaje da hallaka rayukan mutane yayin da suke bacci.
Jaridar ta ce daraktan a hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr. Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da aukuwar lamarin.
Ya ce har yanzu hukumar na ci gaba da tattara bayanai kan girman ɓarnar da ambaliyar ta haddasa, kuma za ta fitar da cikakken rahoto da zarar an kammala bincike.