fidelitybank

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Date:

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun rasa rayukansu sakamakon wata mummunar ambaliya da ta afku a garin Mokwa, hedikwatar karamar hukumar Mokwa da ke jihar Neja.

Mazauna yankin sun bayyana cewa ambaliyar ta katse hanyar da ke hade Arewa da Kudancin Najeriya ta hanyar Mokwa, lamarin da ya jefa matafiya cikin kunci.

Kodayake cikakken bayani bai fito ba tukuna, wasu mazauna yankin sun ce kimanin mutane 50 ne suka rasa rayukansu a musibar.

Har yanzu ana neman wasu mazauna yankin ciki har da mata da ƙananan yara da suka bace. An kuma ruwaito cewa gidaje da dukiyoyi da darajarsu ta kai miliyoyin naira sun nutse sakamakon ambaliyar.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa ambaliyar ta samo asali ne daga ruwan sama mai ƙarfi da aka yi tsawon sa’o’i da dama a daren Laraba, wanda ya yi sanadin nutsewar gidaje da hallaka rayukan mutane yayin da suke bacci.

Jaridar ta ce daraktan a hukumar ba da agajin gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Dr. Ibrahim Audu Hussaini, ya tabbatar da aukuwar lamarin.

Ya ce har yanzu hukumar na ci gaba da tattara bayanai kan girman ɓarnar da ambaliyar ta haddasa, kuma za ta fitar da cikakken rahoto da zarar an kammala bincike.

opra news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naÉ—a Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano É—aure shahararrun...

Rikicinta da Cambodia na iya rikidewa ya koma yaÆ™i – Thailand

Thailand ta gargaÉ—i cewa rikicinta da Cambodia na iya...

Isra’ila da Amurka sun soki Faransa na amincewa da kafuwar Æ™asar FalasÉ—inawa

Isra'ila da Amurka sun yi Allah-wadai da matakin da...

Najeriya za ta kwashe ma’aikatan ta a Congo – Tugar

Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa, ta na shirin kwashe...

Ministan harkokin jin Æ™ai ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC na Æ™asa

Ministan harkokin jin kai, Farfesa Nentawe Yilwatda, ya zama...

Amurka za ta lalata magungunan takarar haihuwa na dala miliyan 10 da za a kawo Afrika

Gwamnatin Amurka na shirin lalata magungunan tazarar haihuwa da...

Hukumar NAFDAC ta kama abubuwan fashewa a Kano

A cewar hukumar, an gano lita 60,000 na sulphuric...

Sojoji sun fafata da da ‘yan Bindiga a Neja

Rundunar sojiji ta ce, sojoji tare da haÉ—in gwiwar...
X whatsapp