fidelitybank

Ambaliya ta raba mutane sama da 50,000 a Kogi

Date:

Sama da mutane 50,000 ne ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu a karamar hukumar Ibaji ta jihar Kogi.

Dan majalisar da ke wakiltar mazabar, Atule Egbunu ya tabbatar da haka a ranar Laraba.

Ya ce kimanin mutane uku ne kuma suka mutu a bala’in yayin da daukacin karamar hukumar ta nutse da ruwa.

A cewar Egbunu, dubban gidaje da filayen noma ne bala’in ya rutsa da su a cikin ruwa wanda ya bayyana a matsayin ” bala’in rashin sa’a na shekara-shekara.”

Ya kuma bayyana bala’in a matsayin mai barna, yana mai cewa mayar da wadanda abin ya shafa zuwa wuri mafi aminci kamar Idah yana da wahala a halin yanzu kuma ya wuce karfin wadanda abin ya shafa.

Dan majalisar ya bayyana cewa a halin yanzu mutanen ba su da abin da ya kamata don magance barnar da bala’in ya janyo, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da sauran kasashen duniya da su kawo musu dauki.

Ya kuma roki gwamnatin jihar da ta gaggauta kai dauki ga al’ummar Ibaji musamman wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...
X whatsapp