Sama da mutane 50,000 ne ambaliyar ruwa ta raba da muhallansu a karamar hukumar Ibaji ta jihar Kogi.
Dan majalisar da ke wakiltar mazabar, Atule Egbunu ya tabbatar da haka a ranar Laraba.
Ya ce kimanin mutane uku ne kuma suka mutu a bala’in yayin da daukacin karamar hukumar ta nutse da ruwa.
A cewar Egbunu, dubban gidaje da filayen noma ne bala’in ya rutsa da su a cikin ruwa wanda ya bayyana a matsayin ” bala’in rashin sa’a na shekara-shekara.”
Ya kuma bayyana bala’in a matsayin mai barna, yana mai cewa mayar da wadanda abin ya shafa zuwa wuri mafi aminci kamar Idah yana da wahala a halin yanzu kuma ya wuce karfin wadanda abin ya shafa.
Dan majalisar ya bayyana cewa a halin yanzu mutanen ba su da abin da ya kamata don magance barnar da bala’in ya janyo, yana mai kira ga gwamnatin tarayya da sauran kasashen duniya da su kawo musu dauki.
Ya kuma roki gwamnatin jihar da ta gaggauta kai dauki ga al’ummar Ibaji musamman wadanda ambaliyar ruwa ta shafa.