Akalla mutane 24 ne suka mutu tare da lalata gidaje 16,625 a jihar Katsina sakamakon ambaliyar ruwa da iska.
An samu rahoton bala’in a lokacin damina ta 2022 a fadin kananan hukumomi 34 na jihar inda aka ce mutane da dama sun samu raunuka daban-daban.
Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na hukumar Umar Muhammad, ta ce adadin gonaki 1,620 ne suka nutse a kananan hukumomin Danja, Ingawa da Kafur na jihar.
Ya ce an lalata kadarori da amfanin gona da aka yi kiyasin asarar miliyoyin naira sakamakon bala’in.
Muhammad ya bayyana cewa hukumar ta tantance gidaje da gonakin da abin ya shafa domin taimakawa wadanda abin ya shafa.
Ya kara da cewa nan ba da jimawa ba gwamnatin jihar za ta fara rabon kayan agaji ga wadanda abin ya shafa.
Gidan Talabijin na Channels Television ya ruwaito a ranar 5 ga Satumba, 2022 cewa, an ce jimillar gidaje 3,813 sun lalace, yayin da mutane biyar suka mutu sakamakon ruwan sama da aka yi a baya-bayan nan a Katsina.