fidelitybank

Ambaliya: Majalisar wakilai ta bukaci Buhari ya kara Naira biliyan 100 a kan kasafi

Date:

Majalisar wakilai ta bukaci shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya mika bukatar naira biliyan 100 domin magance matsalar ambaliyar ruwa.

‘Yan majalisar sun yanke wannan kudurin ne a ranar Litinin din da ta gabata yayin zaman majalisar bayan kudirin muhimmanci ga jama’a da Henry Nwawuba da Isiaka Ibrahim suka gabatar.

Sun bukaci Buhari ya gabatar da karin kasafin kudi na Naira biliyan 100, yayin da suka kuma umarci kwamitin kasafin kudi na majalisar ya sanya Naira biliyan 200 a cikin kasafin kudin 2023.

Bugu da kari, majalisar ta kuma umurci ma’aikatar kudi da ofishin akanta janar na tarayya da su fitar da Naira biliyan 5 domin gudanar da ayyukan kula da muhalli domin dakile illar ambaliyar ruwa.

Da yake gabatar da kudirin, Nwawuba ya ce kasar na fuskantar barazanar karancin abinci idan gwamnati ta kasa daukar matakin da ya dace ta hanyar sa baki a tsanake.

Ya bayyana cewa ambaliyar ta shafi farashin wasu kayayyakin amfanin gona. Ya yi gargadin cewa za a iya shafar wasu masana’antu.

“A shekarar 2012, jahohi 32 cikin 36 da ambaliyar ruwa ta shafa, inda mutane 363 suka mutu, sama da miliyan 2.1 kuma suka rasa matsugunansu, kimanin Naira miliyan 7 ne abin ya shafa, sannan an samu asarar rayuka na Naira tiriliyan 2.6.

“A shekarar 2022, jihohi 33 daga cikin 36 da babban birnin tarayya abin ya shafa, wato kashi 92% na kasar baki daya, sama da mutane 600 ne suka mutu. Sama da mutane miliyan 1.4 ne suka rasa matsugunansu sannan sama da mutane miliyan 2.5 na bukatar agajin jin kai inda sama da kashi 60% na wannan adadin yara ne,” in ji shi.

‘Yan majalisar ne suka amince da kudirin.

national tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp