fidelitybank

Ambaliya: Amurka za ta baiwa Najeriya tallafin dala miliyan 1

Date:

Gwamnatin Amurka za ta bayar da taimakon da ya kai na dala miliyan 1 ga mutanen da ambaliya ta yi wa barna a Najeriya.

Tallafin da za ta bayar ta hanyar hukumarta ta raya kasashe masu tasowa (USAID), zai kasance na gaggawa.

Ruwan sama mai tsanani da ya haddasa ambaliya ya janyo illa ga kusan mutum miliyan 2.8 a fadin kasar.

Gidaje da dama sun lalace ko ma sun rushe a sanadiyyar matsalar wadda ta tashi miliyoyin mutane daga gidajensu.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da ofishin jakadancin Amurkar ya fitar a Abuja a yau Alhamis.

Amurkar ta kuma ce ta damu da yuwuwar ruwan ambaliyar da ya taru a wurare zai iya kara hadarin kamuwa da cutar amai da gudawa da sauran cutuka da ake dauka a ruwa, a jihohin Adamawa da Borno da Yobe.

A wadannan jihohin an samu barkewar cutar kwalara a watan Agusta da Satumba, kuma ta kama mutum akalla 7,750 in ji sanarwar.

A wannan shekarar da ake ciki an samu rahotannin bullar cutar ta amai da gudawa a jihohi 31 daga cikin 36 na Najeriyar.

jakadiyar Amurkar a Najeriya Mary Beth Leonard, ta ce suna cike da jimami kan wadanda ambaliyar ta shafa da suka rasa abubuwa da dama – hanyoyin rayuwarsu da gidajensu har ma da ‘yan uwansu.

Ta kara da cewa Amurka za ta ci gaba da kasancewa tare da al’ummar Najeriya a wannan mawuyacin lokaci.

Sannan za ta yi aiki tare da hukumomin kasar yayin da ake sa ran samun karin ruwan sama da ambaliya a watan Nuwamba, a wasu sassan kasar saboda sauyin yanayi da rashin magudanun ruwa, da nufin samar da karin taimako idan akwai bukatar haka.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp