fidelitybank

Ambaliya a jihar Kogi ya raba sama da mutane 60

Date:

Ambaliya ta ɗaiɗaita al’ummomi sama da 60 a karamar hukumar Ibaji na jihar Kogi.

Da yake tattaunawa da manema labarai, shugaban al’ummar yankin, ya ce lamarin ya yi munin gaske, inda ya yi kira ga gwamnatin jihar ta Kogi da ta ɗauki mataki nan take don shawo kan ambaliyar.

“Ruwa ya ci al’ummomi sama da 60 da ke yankin a halin yanzu,” in ji shi.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Ibaji na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomin jihar da ke fuskantar mummunar ambaliya a kowace shekara.

Ita ma shugabar wani kwamiti cikin ƙungiyar al’ummar yankin, Farfesa Joy Ede ta yi kiran kai musu ɗaukin gaggawa, ciki har da kirkiro da wani asusun tallafi domin taimakawa al’ummomin da ambaliyar ta shafa.

A cewarta, yawan ambaliyar da al’ummomin yankin suka fuskanta musamman waɗanda ke zaune kusa da Kogin Neja, ya fi karfin gwamnatin jihar ita kaɗai har sai an samu ƙarin taimako.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp