fidelitybank

Amarya ta mutu a ranar da aka daura aurenta

Date:

Rahotanni  na nuni da cewa tuni a ka yi jana’izar Amaryar da aka yi auren ta rasu bayan daurin aurenta a jihar Kano.

Amaryar mai suna Hannatu Yahaya ‘yar kimanin shekara 28 ta rasu a ranar daurin aurenta a unguwar Kawon Mai Gari a jihar Kano.

Da ya ke ganawa da manema labarai, dan uwanta, Ayyuba Yahaya, ya ce” Marigayiyar ba ta da tarihin wata rashin lafiya sai makonni biyu da suka gabata, kuma ni ne babban yayan Hannatu, ta yi fama da gajeriyar rashin lafiya na sati biyu kafin bikinta, amma ta samu lafiya ko a ranar daurin aurenta,kuma wannan nufi ne na Allah kawai, kuma mun dauke shi a matsayin kaddara”. A cewar Ayuba.

Malam Yahaya Abagah shi ne mahaifin marigayiyar, ya yi mata addu’a ya mika lamarin ga mahaliccinta.“Allah ya na son ta fiye da mu, shi ne ya ba mu Hannatu, kuma yanzu ya sake kiranta. Ba abin da za mu iya yi da ya wuce kamar cigaba da yi mata addu’a. A takaice dai; ciwon ciki ta samu sati biyu da suka wuce, yawanci yakan je ya dawo mata, wani lokacin idan ciwon cikin ya tashi yana sanya ya kumbura”.

Ba mu iya tantancewa tare da tabbatar da ainihin abin dake faruwa ba, har mutuwar ta. Sa dai gwajin likitoci ya ce Ulcer ne yayin da wani gwajin ya nuna cewa typhoid ne.

An dai daura auren marigayiya Hannatu da angonta Isyaka Yusuf a masallacin Bulama dake Kano a ranar Asabar.

thisday newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp