Rahotanni na nuni da cewa tuni a ka yi jana’izar Amaryar da aka yi auren ta rasu bayan daurin aurenta a jihar Kano.
Amaryar mai suna Hannatu Yahaya ‘yar kimanin shekara 28 ta rasu a ranar daurin aurenta a unguwar Kawon Mai Gari a jihar Kano.
Da ya ke ganawa da manema labarai, dan uwanta, Ayyuba Yahaya, ya ce” Marigayiyar ba ta da tarihin wata rashin lafiya sai makonni biyu da suka gabata, kuma ni ne babban yayan Hannatu, ta yi fama da gajeriyar rashin lafiya na sati biyu kafin bikinta, amma ta samu lafiya ko a ranar daurin aurenta,kuma wannan nufi ne na Allah kawai, kuma mun dauke shi a matsayin kaddara”. A cewar Ayuba.
Malam Yahaya Abagah shi ne mahaifin marigayiyar, ya yi mata addu’a ya mika lamarin ga mahaliccinta.“Allah ya na son ta fiye da mu, shi ne ya ba mu Hannatu, kuma yanzu ya sake kiranta. Ba abin da za mu iya yi da ya wuce kamar cigaba da yi mata addu’a. A takaice dai; ciwon ciki ta samu sati biyu da suka wuce, yawanci yakan je ya dawo mata, wani lokacin idan ciwon cikin ya tashi yana sanya ya kumbura”.
Ba mu iya tantancewa tare da tabbatar da ainihin abin dake faruwa ba, har mutuwar ta. Sa dai gwajin likitoci ya ce Ulcer ne yayin da wani gwajin ya nuna cewa typhoid ne.
An dai daura auren marigayiya Hannatu da angonta Isyaka Yusuf a masallacin Bulama dake Kano a ranar Asabar.