fidelitybank

Amarya ta mutu a ranar da aka daura aurenta

Date:

Rahotanni  na nuni da cewa tuni a ka yi jana’izar Amaryar da aka yi auren ta rasu bayan daurin aurenta a jihar Kano.

Amaryar mai suna Hannatu Yahaya ‘yar kimanin shekara 28 ta rasu a ranar daurin aurenta a unguwar Kawon Mai Gari a jihar Kano.

Da ya ke ganawa da manema labarai, dan uwanta, Ayyuba Yahaya, ya ce” Marigayiyar ba ta da tarihin wata rashin lafiya sai makonni biyu da suka gabata, kuma ni ne babban yayan Hannatu, ta yi fama da gajeriyar rashin lafiya na sati biyu kafin bikinta, amma ta samu lafiya ko a ranar daurin aurenta,kuma wannan nufi ne na Allah kawai, kuma mun dauke shi a matsayin kaddara”. A cewar Ayuba.

Malam Yahaya Abagah shi ne mahaifin marigayiyar, ya yi mata addu’a ya mika lamarin ga mahaliccinta.“Allah ya na son ta fiye da mu, shi ne ya ba mu Hannatu, kuma yanzu ya sake kiranta. Ba abin da za mu iya yi da ya wuce kamar cigaba da yi mata addu’a. A takaice dai; ciwon ciki ta samu sati biyu da suka wuce, yawanci yakan je ya dawo mata, wani lokacin idan ciwon cikin ya tashi yana sanya ya kumbura”.

Ba mu iya tantancewa tare da tabbatar da ainihin abin dake faruwa ba, har mutuwar ta. Sa dai gwajin likitoci ya ce Ulcer ne yayin da wani gwajin ya nuna cewa typhoid ne.

An dai daura auren marigayiya Hannatu da angonta Isyaka Yusuf a masallacin Bulama dake Kano a ranar Asabar.

taraba news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp